ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zaɓen 2027: ADC Ta Yi Alƙawarin Kawo Ƙarshen Rashin Tsaro A Arewa Maso Yamma

by Leadership Hausa
5 months ago

Daga Shehu Yahaya

Jam’iyyar adawa ta ADC a shiyyar Arewa maso Yamma ta kara jadadda kudirinta na magance matsalar rashin tsaro da ke addabar yankin, idan har ta samu damar rike madafun iko a zabukan shekarar 2027 masu zuwa.

 

Mataimakin Shugaban Jam’iyyar ADC na kasa mai wakiltar shiyyar Arewa maso Yamma, Malam Jafaru Sani, ne ya bayyana hakan yayin wata tattaunawa da wakilinmu a Kaduna, jim kadan bayan kammala wani babban taron jam’iyyar da aka gudanar a jihar.

ADVERTISEMENT
  • Hukumar Kula Da Alkalai Ta Haramta Wa Lauyoyi 34 Zama Masu Shari’a A Nijeriya
  • Dalilin Ɗage Sauya Sheƙar Gwamna Abba Kabir Yusuf Zuwa 12 Ga Janairu

Malam Jafaru Sani ya ce jam’iyyar ADC tana da tsare-tsare masu inganci da za su taimaka wajen shawo kan matsalar rashin tsaro a yankin Arewa maso Yamma da ma kasa baki daya, tare da kawo gyara a bangaren harkokin shari’a domin tabbatar da adalci da zaman lafiya.

 

LABARAI MASU NASABA

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Ya kara da cewa lokaci ya yi da al’ummar Nijeriya za su rungumi sabuwar tafiya da hadakar jam’iyyar ADC, domin ceto kasar nan daga mawuyacin halin da take ciki, wanda ya alakanta da gazawar jam’iyyar APC mai mulki.

 

A cewarsa, ADC jam’iyya ce da ke da hangen nesa, manufofi na gaskiya, da jajircewar shugabanni da za su iya kawo sauyi mai ma’ana ga rayuwar ‘yan Nijeriya, musamman a fannonin tsaro, tattalin arziki da adalci.

 

Jam’iyyar ADC ta yi kira ga al’ummar Arewa maso Yamma da su hada kai da jam’iyyar domin gina kasa mai inganci, tsaro da ci gaba mai dorewa a nan gaba.

 

Shugaban yace jam’iyyar APC mai mulki ta gaza wajen kare rayuka da dukiyoyin ‘yan kasa, tare da kasa cika alkawuran da ta dauka ga al’umma tun bayan hawanta mulki.

 

Malam Jafaru Sani ya jaddada cewa ADC jam’iyya ce da ke da nagartattun shugabanni, manufofi masu ma’ana da kuma tsari mai karfi da zai iya kawo sahihin sauyi a Najeriya, musamman a fannoni irin su tsaro, tattalin arziki, ilimi da shari’a..

 

Hakazalika, yayi kira ga al’ummar Arewa Maso Yamma da su mara mata baya domin samar da tsaro, adalci da ci gaba mai dorewa a Nijeriya.

Leadership Hausa
Website |  + postsBio
  • Leadership Hausa
    Yadda Arsenal Ta Lashe Gasar Firimiya Bayan Shekara 22
  • Leadership Hausa
    Bukatar Kawo Karshen Akidar Kyamar Baki A Kasar Afirka Ta Kudu
  • Leadership Hausa
    Ikirarin Cewa Sanata Abdul’aziz Yari Abubakar, Marafan Sokoto, Nauyi Ne Ga Jihar Zamfara Da Jam’iyyar APC Ba Ta Da Tushe
  • Leadership Hausa
    Nazarin Kisan Gillar Da ‘Yan Kato Da Gora Suka Yi Wa Wani Matashi A Biniwe

MASU ALAKA

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi
Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi
Manyan Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna
Labarai

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Next Post
Lee Jae-Myung: Tabbas Za A Kyautata Hulda Tsakanin Koriya Ta Kudu Da Sin

Lee Jae-Myung: Tabbas Za A Kyautata Hulda Tsakanin Koriya Ta Kudu Da Sin

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.