ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, September 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zaɓen 2027: ADC Ta Yi Alƙawarin Kawo Ƙarshen Rashin Tsaro A Arewa Maso Yamma

by Leadership Hausa
8 months ago

Daga Shehu Yahaya

Jam’iyyar adawa ta ADC a shiyyar Arewa maso Yamma ta kara jadadda kudirinta na magance matsalar rashin tsaro da ke addabar yankin, idan har ta samu damar rike madafun iko a zabukan shekarar 2027 masu zuwa.

 

Mataimakin Shugaban Jam’iyyar ADC na kasa mai wakiltar shiyyar Arewa maso Yamma, Malam Jafaru Sani, ne ya bayyana hakan yayin wata tattaunawa da wakilinmu a Kaduna, jim kadan bayan kammala wani babban taron jam’iyyar da aka gudanar a jihar.

ADVERTISEMENT
  • Hukumar Kula Da Alkalai Ta Haramta Wa Lauyoyi 34 Zama Masu Shari’a A Nijeriya
  • Dalilin Ɗage Sauya Sheƙar Gwamna Abba Kabir Yusuf Zuwa 12 Ga Janairu

Malam Jafaru Sani ya ce jam’iyyar ADC tana da tsare-tsare masu inganci da za su taimaka wajen shawo kan matsalar rashin tsaro a yankin Arewa maso Yamma da ma kasa baki daya, tare da kawo gyara a bangaren harkokin shari’a domin tabbatar da adalci da zaman lafiya.

 

LABARAI MASU NASABA

Jerin Bankuna 32 Da Aka Amince Su Sayar Da Hannun Jarin Matatar Dangote

Uganda Za Ta Fara Fitar Da Man Fetur Zuwa Ƙasashen Waje

Ya kara da cewa lokaci ya yi da al’ummar Nijeriya za su rungumi sabuwar tafiya da hadakar jam’iyyar ADC, domin ceto kasar nan daga mawuyacin halin da take ciki, wanda ya alakanta da gazawar jam’iyyar APC mai mulki.

 

A cewarsa, ADC jam’iyya ce da ke da hangen nesa, manufofi na gaskiya, da jajircewar shugabanni da za su iya kawo sauyi mai ma’ana ga rayuwar ‘yan Nijeriya, musamman a fannonin tsaro, tattalin arziki da adalci.

 

Jam’iyyar ADC ta yi kira ga al’ummar Arewa maso Yamma da su hada kai da jam’iyyar domin gina kasa mai inganci, tsaro da ci gaba mai dorewa a nan gaba.

 

Shugaban yace jam’iyyar APC mai mulki ta gaza wajen kare rayuka da dukiyoyin ‘yan kasa, tare da kasa cika alkawuran da ta dauka ga al’umma tun bayan hawanta mulki.

 

Malam Jafaru Sani ya jaddada cewa ADC jam’iyya ce da ke da nagartattun shugabanni, manufofi masu ma’ana da kuma tsari mai karfi da zai iya kawo sahihin sauyi a Najeriya, musamman a fannoni irin su tsaro, tattalin arziki, ilimi da shari’a..

 

Hakazalika, yayi kira ga al’ummar Arewa Maso Yamma da su mara mata baya domin samar da tsaro, adalci da ci gaba mai dorewa a Nijeriya.

Leadership Hausa
Website |  + postsBio
  • Leadership Hausa
    Wane Ne Dan Shagamu: Su Wane Ne Suka Kashe Shi A Kano?
  • Leadership Hausa
    An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu
  • Leadership Hausa
    Karuwar Farin Jinin Gwamna Umaru Bago A Siyasar Jihar Neja
  • Leadership Hausa
    Kyakkyawan Tsarin Laken Asiri Zai Dakile Shirin Magudin Zabe A Nijeriya —Mohammed

MASU ALAKA

Labarai

Jerin Bankuna 32 Da Aka Amince Su Sayar Da Hannun Jarin Matatar Dangote

September 10, 2026
Labarai

Uganda Za Ta Fara Fitar Da Man Fetur Zuwa Ƙasashen Waje

September 10, 2026
Cutar Mashaƙo Ta Ɓarke A Kano, Katsina Da Filato
Manyan Labarai

Mashaƙo: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Sun Kai 27 A Filato

September 10, 2026
Next Post
Lee Jae-Myung: Tabbas Za A Kyautata Hulda Tsakanin Koriya Ta Kudu Da Sin

Lee Jae-Myung: Tabbas Za A Kyautata Hulda Tsakanin Koriya Ta Kudu Da Sin

LABARAI MASU NASABA

Jerin Bankuna 32 Da Aka Amince Su Sayar Da Hannun Jarin Matatar Dangote

September 10, 2026

Uganda Za Ta Fara Fitar Da Man Fetur Zuwa Ƙasashen Waje

September 10, 2026
Cutar Mashaƙo Ta Ɓarke A Kano, Katsina Da Filato

Mashaƙo: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Sun Kai 27 A Filato

September 10, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

Wane Ne Dan Shagamu: Su Wane Ne Suka Kashe Shi A Kano?

September 10, 2026
Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara

Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara

September 10, 2026
Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

September 10, 2026
’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya

’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya

September 10, 2026
2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

September 10, 2026
Zabe: Gwamnatin Kano Ta Taƙaita Zirga-zirgar Mutane Da Ababen Hawa

Gwamna Yusuf Ya Umarci Jami’an Tsaro Su Gano Waɗanda Suka Kashe Danshagamu

September 10, 2026
Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

September 9, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.