Alamun rikicin siyasa na ƙara bayyana a Jihar Kano gabanin zaɓen 2027, yayin da rahotanni ke nuni da cewa tsohon Mataimakin Gwamnan jihar, Abdullahi Tijjani Muhammad Gwarzo, na shirin kalubalantar Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Barau I. Jibrin, a takarar Sanatan Kano ta Arewa.
Rahotanni sun bayyana cewa wannan yunƙuri na iya haifar da gagarumin fafatawar siyasa a tsakanin manyan ‘yan siyasa a jihar, musamman duba da muhimmancin Kano a siyasar ƙasa
Sanata Barau, wanda ke wakiltar Kano ta Arewa a Majalisar Dattawa tun shekarar 2015, ana kallonsa a matsayin ɗaya daga cikin manyan jiga-jigan jam’iyyar APC a jihar.
A nasa ɓangaren, Gwarzo na da tasiri a siyasar Kano, musamman saboda alaƙarsa da manyan jagororin siyasa da kuma goyon bayan da yake samu a tsakanin al’umma.
Masu nazarin siyasa na ganin cewa wannan fafatawa na iya zama babbar gwagwarmaya tsakanin ɓangarorin siyasar jihar, wadda za ta iya sauya fasalin siyasar Kano kafin zaɓen 2027.
Sun kuma jaddada cewa yadda jam’iyyun siyasa za su tsara kansu da kuma irin haɗin gwiwar da za a samu tsakanin ‘yan siyasa zai taka muhimmiyar rawa wajen tantance wanda zai yi nasara.
A halin yanzu, ana ci gaba da sa ido kan yadda al’amura za su gudana, yayin da shirye-shiryen zaɓen 2027 ke ƙara ɗaukar zafi.















Discussion about this post