ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zumunci Da Hadin Kan Marubuta Na Matukar Burge Ni – Manab ‘Yar Baba

by Rabi'at Sidi Bala
3 years ago
Manab

Matashiyar marubuciya da tauraronta ke haskawa a duniyar marubutan yanar gizo, Minab ‘Yar Baba ta bayyana jin dadi da farin cikinta yadda marubutan suke mu’amalantar juna tamkar ‘yan uwan da suke ahali daya ba tare da nuna bambanci tsakaninsu ba.

Wanda a cewarta hakan wani sirri ne daga sirrikan bunkasar rubutu da marubutan Hausa a fadin duniya. Ga dai yadda tattaunawarta ta kasance tare da wakilinmu, Adamu Yusuf Indabo:

Wace ce Manab ‘Yar Baba?
To da farko dai cikakken sunana shi ne Maryam Nasir Ibrahim, wadda a duniyar rubutu aka fi sanina da Manab ‘Yar Baba. An haife ni a garin Kano ce, na yi karatuna na bangaren addini da boko duka a nan birnin Kano.

ADVERTISEMENT

To ta ya kika tsinci kanki a duniyar rubutu?
Rubutu wani abu ne da na taso da shaukinsa, tun a lokacin ban fahimci me ake nufi da rubutu ba ko nake jagwalgwalona da sunan rubutu. Na fara rubutu tun ina JS 1 a edercise book, zan zauna na rubuta, na kuma tara classmates ina karanta musu, ko kuma na ba su labari ba tare da na rubuta ba. Daga baya na fara rubutu a online a lokacin da ban zata ko shiryawa hakan ba. Shigata duniyar rubutu ya samo asali ne da karfin gwiwa da na samu, wanda har yanzu ba zan iya mantawa da hakan ba.

Yaushe kika fara rubutu, zuwa yanzu kin rubuta littafai nawa?
Na fara rubutu a ranar wata Talata da ta yi daidai Shida ga watan Takwas a shekarar Dubu Biyu Da Shatara (06/08/2019). Littafina na farko da na rubuta shi ne MONAH. Amma yanzu haka na rubuta littafai guda Bakwai (7) su ne:Monah, Iya Ruwa, Kanin Ajali, Jannat, Madafa, Laifin Waye? Da kuma Sai Na Dauki Fansa. Amma shi sai na dauki fansa na hadin gwiwa ne.

LABARAI MASU NASABA

Tun Ina Karama Marigayi Tumbuleke Ke Sa Ni Dariya —Hannatu Musawa

Nazari Kan Wasu Dalilan Da Ke Haddasa Sabanin Abotakar Jarumi Ko Jaruma A Kannywood

To cikin wadannan littafai guda 7 wanne bakandamiyarki?
JANNAT shi ne bakandamiyata. Saboda cikinsa akwai babban lamari da ya bambanta shi da sauran littafaina. Labarin Jannat labari ne da na gina sa a kan nuni da wasu halayya da suke da matsala a rayuwa, kamar munafurci, hassada da kyashi, karya da dai sauransu. Amma jigon labarin shi ne nuni da nusar da illar son kai, a ta wani bangaren kuma soyayya. Kuma da yawan labarin abubuwa ne da suka faru a gaskiyance. Shi ya sa lokacin da nake rubutunsa na jingine komai na tattara hankalina gare sa. Kuma Alhamdulillah! Ya samu karbuwan da ban yi tunanin haka ba.

To cikin littafan kuma wanne ya fi ba ki wahala wajen rubutunsa?
MADAFA ya fi ba ni wahala, dan na ma a jesa a gefe guda, har yau na kasa kammala sa. Wani lokaci nakan dauko shi kamar zan ci gaba amma sai lamarin ya citira. Saboda al’adun mutanen ciki, da ratuwarsu. Domin magana ce da ake ta shudaddan lokaci, karni Uku da ya wuce. Shi ya sa yake da wahala, dole sai da bincike a kai, domin komai na lokacin da ne, wanda yake daban da na yanzu.

Cikin wanne irin yanayi kika fi jin dadin yin rubutu?
A yanayi na kadaici, na fi jin dadin yin rubutu a lokacin.

Daga fara rubutunki zuwa yau, wanne nasarori kika cimma ta sanadin rubutu?
Alhamdulillah! Daidai gwargwado na samu nasarori sanadiyar rubutu, ko bangaren ilimi ma na san nasara ce, dan akwai abubuwa da yawan da sanadin rubutu na san su.

Ya batun kalubale?
Kalubale! Tam ita rayuwa dama ta gaji haka, idan kana abu ba ka samu kalubale ba a kansa kai karan kanka sai ka tsargu, sai dai kuma in ka ce za ka mayar da hankali a kan haka, to ba za ka taba gaba ba, dan kwan gaba kwan baya mutum zai ta yi. Alhamdulillah ni kalubalen da na fuskanta sun zame min alkhairi a gare ni, domin ana daukar darasi ne daga kuskure.

Wanne sako kike da shi ga masoyanki?
Sakona ga masoya a ina matukar godiya da kaunarku a gare ni, ku ne karfin gwiwata, ina yi muku fatan alkhairi a rayuwarku.

‘Yan uwanki marubuta, wanne kira za ki yi gare su?
Marubuta! Bayin Allah! Hakika kuna himdimtawa al’umma ta hanyar ilimantar da su tare da nishadantarwa da kuma fadakarwa, Allah ya yi mana jagora. Sai dai ina kira da baragurbin marubuta da dan Allah su dakata haka nan, su tsaftace al’kalumansu da tunaninsu, domin rubutu tunanin marubuci ne. Sannan mu tuna abu biyu, na farko sau tari makaranci ya na daukar tunanin marubuci, ya ce zai yi amfani da shi a duniyarmu ta zahiri, ka ga ke nan rubutu yana zama silar gyara da kuma bata tarbiya, in rubutunki/ka ya zama silar gyara to kina/kana da lada, in kuma akasin haka ne shi ma haka ne. Na biyu a duk lokacin da muka rubuta kalma daya mu tuna da sai fa an tambaye mu a ranar da bakinmu ba zai magana ba. Sannan sai dan wani abu da nake son magana a kansa, dan Allah kafin mu rubuta mu san mene ne ake nufi da rubutu? Ya ake yin rubutun nan? Mene ne ka’idojin rubutu? Da dai sauransu.

A karshe ina mika sakon girmamawa da gaisuwa ga manyan da kananan marubuta, da fatan Allah ya yi mana jagora ya kiyaye mana alkalumanmu ga janyo mu ga halaka. Kuma ya bar mana zumuncinmu, domin zumunci da hadin kan marubuta na matukar burge ni.

Hajiya Manab ‘Yar Baba muna godiya.
Ni ma na gode sosai da wannan damar.

Manab
Rabi'at Sidi Bala
+ postsBio
  • Rabi'at Sidi Bala
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiat-sidi-bala/
    Yadda Alaƙata Da Adamu Zango Ta Bunƙasa A Kannywood —Jarumi Ibrahim Sodangi 
  • Rabi'at Sidi Bala
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiat-sidi-bala/
    Fim Ko Gaske:Yaushe Masu Kallon Fina-finai Za Su Daina Daukar Fim A Matsayin Gaske
  • Rabi'at Sidi Bala
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiat-sidi-bala/
    Fim ɗin ƙaddara: Anya Ana Samun Irin Wannan ƙaddarar Kuwa?
  • Rabi'at Sidi Bala
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiat-sidi-bala/
    Ko Kafa Ƴansandan Jihohi Zai Taimaka Wajen Kawo Ƙarshen Matsalolin Tsaro?

MASU ALAKA

Tun Ina Karama Marigayi Tumbuleke Ke Sa Ni Dariya —Hannatu Musawa
Nishadi

Tun Ina Karama Marigayi Tumbuleke Ke Sa Ni Dariya —Hannatu Musawa

September 5, 2026
Nazari Kan Wasu Dalilan Da Ke Haddasa Sabanin Abotakar Jarumi Ko Jaruma A Kannywood
Nishadi

Nazari Kan Wasu Dalilan Da Ke Haddasa Sabanin Abotakar Jarumi Ko Jaruma A Kannywood

August 29, 2026
Manab
Nishadi

Dalilan Da Suka Sa Ba Zan Iya Auren Ɗan Film Ba —Bilkisu Bishasha

August 23, 2026
Next Post
Yanzu-yanzu: Jirgin Max Air Ya Yi Hatsari A Filin Jirgin Saman Abuja

Yanzu-yanzu: Jirgin Max Air Ya Yi Hatsari A Filin Jirgin Saman Abuja

LABARAI MASU NASABA

Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.