Ƙungiyar ‘yan majalisar jam’iyyar ADC ta yi kakkausar suka ga matakin Shugaban Ƙasa Bola Tinubu na neman amincewar Majalisar Dattawa domin karɓo sabon bashi a ƙasar waje na dala miliyan 516,333,070 don aikin titin Sokoto–Badagry. Bukatar ta fito ne cikin wasiƙar da aka karanta a zauren majalisar ranar Alhamis, inda aka nemi izini bisa tanadin dokar Debt Management Office ta 2011.
Shugaban ƙungiyar, Hon. Uko Ndukwe Nkole, tare da shugabannin yankuna, sun bayyana cewa wannan mataki abin damuwa ne, suna zargin gwamnati da mayar da karɓo bashi wata hanya ta yau da kullum ba tare da la’akari da ɗorewa da jin daɗin al’umma ba. Sun kuma ce duk da muhimmancin ayyukan more rayuwa, ya kamata a fayyace tsadar aiki da sharuɗɗan bashin.
A cewarsu, gwamnatin ba ta gabatar da ingantaccen tsari na biyan bashin ko hujjoji masu gamsarwa kan yadda ake sarrafa basussukan ba. Sun ce Nijeriya na fuskantar nauyin bashi mai yawa, inda biyan bashi ke cin kaso mai tsoka na kuɗaɗen shiga, amma duk da haka ana ci gaba da ƙara zurfafa cikin matsalar tattalin arziƙi.
Ƙungiyar ta buƙaci Majalisar Dattawa da kada ta zama ƴar amshin shatan, ya kamata tana neman cikakken bayani kan aiki, da tsarin kashe kuɗi da yadda za a biya bashin.
Haka kuma ta shawarci gwamnati da ta mai da hankali kan manufofin da za su bunƙasa tattalin arziƙi, samar da ayyukan yi da rage asarar kuɗaɗen shiga, tana gargaɗin cewa al’umma za su nemi jin bahasi kan duk wani mataki da zai jefa ƙasar cikin matsalar tattalin arziƙi.















Discussion about this post