Jam’iyyar hadaka ta ADC ta caccaki Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu bisa zarginsa da karkatar da hankalin al’umma daga matsalar tsaro da ke ta kara tabarbarewa a Nijeriya ta hanyar fara yakin neman sake zabensa a shekarar 2027 tun kafin lokaci ya yi.
Jam’iyyar ta ce matakin ba wai kawai yana lalata lamarin ba ne har ma da ingancin tsaro da shugaban kasa da kansa ya ayyana.
- Tsohon Gwamnan Kaduna, El-Rufai, Ya Fice Daga SDP, Ya Koma ADC
- 2027: Ganduje Ya Gargaɗi Mambobin APC Kan Fara Tallata Masu Neman Takarar Gwamna Da Wuri
A cikin wata sanarwa da sakatare yada labarai na jam’iyyar ADC, Malam Bolaji Abdullahi, ya sanya hannu, jam’iyyar adawa ta yi suka ga rahotannin da ke cewa shugaban kasa ya rarraba motocin da ke da alama ga yada siyasa karkashin shirinsa na ‘Ambassadors na Sabon Fata’ a fadin kasar nan.
Ya yi gargadin cewa irin wannan aiki ya keta jadawalin kamfen din hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) kuma yana kawo damuwa ga tsarin mulki a wannan lokaci.
A cewar Abdullahi, wannan lamari na ci gaba da jefa shakku kan kokarin gwamnati wajen magance rashin tsaro da ke kara ta’azzara wanda ya sa da dama daga cikin ‘yan Nijeriya an yi garkuwa da su da tilasta musu na barin gidajensu da kuma gudanar da rayuwa cikin tsoro.
“Jam’iyyar hadaka ta ADC tana cikin matukar damuwa da rahotannin da ke cewa Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya raba jerin manyan motoci kirar Hilud, Land Cruiser, da motoci masu daukar fasinja kirar Hummer ga wakilan siyasa a fadin kasar nan, ta haka ne ya fara kamfaninsa na neman sake zabensa a 2027,” in ji Abdullahi.
Jam’iyya ta bayyana cewa yayin da kasar ke bukatar karfafa matakan tsaro da mayar da hankali ba tare da jinkiri ba wajen dawo da aminci, amma gwamnati na ci gaba da gudanar da ayyukan siyasa na yau da kullum duk da yadda mawuyacin halin da ‘yan kasa suke ciki.
“Yayin da a kullum ‘yan kasa na fama da matsalar garkuwa da mutane da kashe-kashe da yin kaura a daidai wannan lokaci kuma shugaban kasa ya raba motocin siyasa,” in ji Abdullahi.
ADC ta jaddada cewa kasar na bukatar a dauki matakan gaggawa kan shugabanci, ba kawai gudanar da sha’anin siyasa ba.
Jam’iyyar ta kuma bayyana Tinubu ya zama shugaban Nijeriya na farko da aka zaba da ya ayyana dokar ta-baci kan tsaro, yayin da ake zarginsa fara yakin nema zabe tun kafin lokaci ya yi.
Ya yi kira ga INEC da ta dauki matakan gaggawa don magance abin da ta bayyana a matsayin kararar doka a tsarin zabe.














