ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2027: ADC Ta Caccaki Tinubu Kan Azarbabin Fara Yakin Neman Zabe

by Leadership Hausa
6 months ago
ADC

Jam’iyyar hadaka ta ADC ta caccaki Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu bisa zarginsa da karkatar da hankalin al’umma daga matsalar tsaro da ke ta kara tabarbarewa a Nijeriya ta hanyar fara yakin neman sake zabensa a shekarar 2027 tun kafin lokaci ya yi.

Jam’iyyar ta ce matakin ba wai kawai yana lalata lamarin ba ne har ma da ingancin tsaro da shugaban kasa da kansa ya ayyana.

  • Tsohon Gwamnan Kaduna, El-Rufai, Ya Fice Daga SDP, Ya Koma ADC
  • 2027: Ganduje Ya Gargaɗi Mambobin APC Kan Fara Tallata Masu Neman Takarar Gwamna Da Wuri

A cikin wata sanarwa da sakatare yada labarai na jam’iyyar ADC, Malam Bolaji Abdullahi, ya sanya hannu, jam’iyyar adawa ta yi suka ga rahotannin da ke cewa shugaban kasa ya rarraba motocin da ke da alama ga yada siyasa karkashin shirinsa na ‘Ambassadors na Sabon Fata’ a fadin kasar nan.

ADVERTISEMENT

Ya yi gargadin cewa irin wannan aiki ya keta jadawalin kamfen din hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) kuma yana kawo damuwa ga tsarin mulki a wannan lokaci.

A cewar Abdullahi, wannan lamari na ci gaba da jefa shakku kan kokarin gwamnati wajen magance rashin tsaro da ke kara ta’azzara wanda ya sa da dama daga cikin ‘yan Nijeriya an yi garkuwa da su da tilasta musu na barin gidajensu da kuma gudanar da rayuwa cikin tsoro.

LABARAI MASU NASABA

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

‘Yan Majalisar Wakilai 6 Daga Oyo Sun Fice Daga PDP Zuwa APM

“Jam’iyyar hadaka ta ADC tana cikin matukar damuwa da rahotannin da ke cewa Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya raba jerin manyan motoci kirar Hilud, Land Cruiser, da motoci masu daukar fasinja kirar Hummer ga wakilan siyasa a fadin kasar nan, ta haka ne ya fara kamfaninsa na neman sake zabensa a 2027,” in ji Abdullahi.

Jam’iyya ta bayyana cewa yayin da kasar ke bukatar karfafa matakan tsaro da mayar da hankali ba tare da jinkiri ba wajen dawo da aminci, amma gwamnati na ci gaba da gudanar da ayyukan siyasa na yau da kullum duk da yadda mawuyacin halin da ‘yan kasa suke ciki.

“Yayin da a kullum ‘yan kasa na fama da matsalar garkuwa da mutane da kashe-kashe da yin kaura a daidai wannan lokaci kuma shugaban kasa ya raba motocin siyasa,” in ji Abdullahi.

ADC ta jaddada cewa kasar na bukatar a dauki matakan gaggawa kan shugabanci, ba kawai gudanar da sha’anin siyasa ba.

Jam’iyyar ta kuma bayyana Tinubu ya zama shugaban Nijeriya na farko da aka zaba da ya ayyana dokar ta-baci kan tsaro, yayin da ake zarginsa fara yakin nema zabe tun kafin lokaci ya yi.

Ya yi kira ga INEC da ta dauki matakan gaggawa don magance abin da ta bayyana a matsayin kararar doka a tsarin zabe.

ADC
Leadership Hausa
Website |  + postsBio
  • Leadership Hausa
    Yadda Arsenal Ta Lashe Gasar Firimiya Bayan Shekara 22
  • Leadership Hausa
    Bukatar Kawo Karshen Akidar Kyamar Baki A Kasar Afirka Ta Kudu
  • Leadership Hausa
    Ikirarin Cewa Sanata Abdul’aziz Yari Abubakar, Marafan Sokoto, Nauyi Ne Ga Jihar Zamfara Da Jam’iyyar APC Ba Ta Da Tushe
  • Leadership Hausa
    Nazarin Kisan Gillar Da ‘Yan Kato Da Gora Suka Yi Wa Wani Matashi A Biniwe

MASU ALAKA

Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe
Siyasa

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
‘Yan Majalisar Wakilai 6 Daga Oyo Sun Fice Daga PDP Zuwa APM
Siyasa

‘Yan Majalisar Wakilai 6 Daga Oyo Sun Fice Daga PDP Zuwa APM

June 3, 2026
Gwamnatina Za Ta Mayar Da Hankali Kan Buƙatun Al’ummar Nasarawa – Wadada
Siyasa

Gwamnatina Za Ta Mayar Da Hankali Kan Buƙatun Al’ummar Nasarawa – Wadada

June 1, 2026
Next Post
Dawo Da Martabar Birnin Abuja Ta Hanyar Doka Da Oda Shi Ne Babbar Burin Wike – Mukthar Galadima

Dawo Da Martabar Birnin Abuja Ta Hanyar Doka Da Oda Shi Ne Babbar Burin Wike - Mukthar Galadima

LABARAI MASU NASABA

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.