Hukumar INEC ta ce tana nazarin yiwuwar duba jadawalin babban zaɓen 2027 bayan koke-koken da suka taso kan daidaituwar ranar 20 ga Fabrairu, 2027 da watan azumin Ramadan. Tun da farko, hukumar ta ayyana cewa za a gudanar da zaɓen Shugaban Ƙasa da na Majalisar Tarayya a ranar 20 ga Fabrairu, yayin da na gwamnoni da majalisun jihohi za su gudana a ranar 6 ga Maris, 2027.
Wasu ’yan ƙasa, musamman Musulmi, sun nuna damuwa cewa zaɓe a lokacin azumi na iya shafar fitowar masu kaɗa ƙuri’a da aikin jami’an zaɓe. Cikin masu kira da a sake duba ranar akwai tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Atiku Abubakar, wanda ya ce ranar ta faɗo daidai cikin Ramadan (7 Fabrairu zuwa 8 Maris, 2027). Tsohon hadimin shugaban ƙasa, Bashir Ahmad, shi ma ya buƙaci a sake tunani domin tabbatar da cikakkiyar halartar jama’a.
- Rikicin Cikin Gida Na Jam’iyyun Siyasa Na Yin Mummunan Tasiri Ga Sahihancin Zaben Nijeriya – INEC
- Shehu Sani Ya Yi Allah-Wadai Da Buƙatar Shugaban INEC Ya Sauka
Sai dai INEC, ta bakin Kwamishinan Yaɗa Labarai da Ilimantar da Masu Zaɓe, Mohammed Haruna, ta ce jadawalin ya yi daidai da Kundin Tsarin Mulki na 1999 (da aka yi wa kwaskwarima), Dokar Zaɓe ta 2022 da ƙa’idojin gudanar da zaɓe da suka tanadi cewa zaɓen shugaban ƙasa da na majalisar tarayya su gudana a Asabar ta uku na watan Fabrairu a shekarar zaɓe.
Duk da haka, hukumar ta ce tana sauraron damuwar masu ruwa da tsaki, kuma za ta ci gaba da tuntuɓar ɓangarori daban-daban, tare da yiwuwar neman matakin majalisa idan ya zama dole, domin duk wani sauyi ya kasance cikin iyakar doka. INEC ta jaddada aniyarta na gudanar da zaɓe cikin gaskiya, da haɗin kai da sahihanci.















Discussion about this post