ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Kai Hari Da Jirgin Sama Maras Matuƙi Kan Ofishin Jakadancin Amurka A Baghdad

by Abubakar Sulaiman
3 months ago
Amurka

Wani hari da jirgin sama maras matuƙi ya afkawa ofishin jakadancin Amurka a Baghdad, lamarin da ya sake tayar da hankula a yankin Gabas ta Tsakiya yayin da rikici ke ƙara tsananta tsakanin Amurka, Israel da Iran.

Rahotanni sun ce fashe-fashe sun girgiza wasu birane a yankin a ranar Asabar, yayin da aka kai hari karo na biyu kan ofishin jakadancin Amurka tun daga ranar 28 ga Fabrairu. An kuma ga hayaƙi mai kauri yana tashi daga tashar jiragen ruwa ta Fujairah, ɗaya daga cikin manyan wuraren adanawa da fitar da man fetur a United Arab Emirates.

  • Amurka Ta Yi Watsi Da Nadin Mojtaba Khamenei’ Sabon Shugaban Iran
  • Amurka Ce Tushen Matsalar Da Ake Ciki Dangane Da Batun Nukiliyar Iran

Rikicin ya ƙara tsananta bayan hare-haren jiragen sama marasa matuƙa, da makamai masu linzami da hare-haren sama da aka ruwaito sun yi sanadin mutuwar sama da mutane 1,200 a Iran, a cewar ma’aikatar lafiyar ƙasar. Haka kuma an ce Iran ta kai hare-haren makamai masu linzami da jiragen sama marasa matuƙi kan aƙalla ƙasashe 10 maƙwabta, abin da ya dagula zirga-zirgar jiragen ruwa a mashigar Hormuz.

ADVERTISEMENT

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya tabbatar da cewa sojojin Amurka sun kai hari kan tsibirin Kharg Island, babban cibiyar fitar da man fetur ta Iran, inda aka kai hari kan wuraren soja amma ba a lalata cibiyoyin mai ba.

Rahotanni sun kuma ce tsohon jagoran Iran, Ali Khamenei, ya mutu a farkon hare-haren da Amurka da Isra’ila suka ƙaddamar, yayin da aka naɗa ɗansa Mojtaba Khamenei a matsayin sabon jagoran ƙasar.

LABARAI MASU NASABA

Yara 14 Sun Rasu Sakamakon Gobara A Kudancin Indiya

Amurka Ta Dakatar Da Takunkumin Man Fetur Kan Iran

A cewar babban Jakadan Majalisar Dinkin Duniya kan ƴan gudun hijira, rikicin ya tilasta wa kusan mutane miliyan 3.2 barin gidajensu a Iran. A halin yanzu, Pentagon ya ce sojojin Amurka da Isra’ila sun kai hare-hare fiye da 15,000 a wurare daban-daban a Iran cikin makonni biyu da suka gabata.

Amurka
Abubakar Sulaiman
Website |  + postsBio
  • Abubakar Sulaiman
    Jam’iyyar APC Ta Tafka Asarar Mabiya A Gombe, Sun Bi Pantami PDP
  • Abubakar Sulaiman
    Gwamnatin Tarayya Ta Gargaɗi Masu Ɓoye Gas Ɗin Girki
  • Abubakar Sulaiman
    Kotu Ta Bayar Da Umarnin Tsare Sowore A Gidan Yarin Kuje
  • Abubakar Sulaiman
    Yanzu-Yanzu: An Kashe Manoma 18 Da Raunata Wasu A Wani Sabon Hari A Filato

MASU ALAKA

Yara 14 Sun Rasu Sakamakon Gobara A Kudancin Indiya
Kasashen Ketare

Yara 14 Sun Rasu Sakamakon Gobara A Kudancin Indiya

June 23, 2026
Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya
Kasashen Ketare

Amurka Ta Dakatar Da Takunkumin Man Fetur Kan Iran

June 22, 2026
Sin Ta Yi Maraba Da Yarjejeniyar Fahimtar Juna Da Aka Cimma Tsakanin Amurka Da Iran
Kasashen Ketare

Iran Ta Ce Shirinta Na Makamai Masu Linzami Ba Ya Cikin Tattaunawa Da Amurka

June 18, 2026
Next Post
Wane Irin Tanadi Kuka Yi Wa Sallah Karama A Wannan Lokacin?

Wane Irin Tanadi Kuka Yi Wa Sallah Karama A Wannan Lokacin?

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026
Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

June 23, 2026
Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

June 23, 2026
Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.