Shugabannin jam’iyyar Nigeria NDC na karɓar baƙuncin Peter Obi da Rabiu Musa Kwankwaso a wani muhimmin taro da ke gudana a Abuja.
Taron na samun halartar shugaban jam’iyyar na ƙasa, Moses Cleopas, da kuma jagoran jam’iyyar, Seriake Dickson, yayin da ake ci gaba da tattaunawa kan yiwuwar sauya sheƙar manyan ‘yan siyasar biyu.
Obi da Kwankwaso, waɗanda suka zo na uku da na hudu a zaɓen shugaban ƙasa da ya gabata, na shirin ficewa daga jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) bayan shiga wani ƙawance na siyasa da nufin ƙalubalantar shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu.
Rahotanni sun nuna cewa rikicin shugabanci da matsalolin shari’a da ke addabar ADC, ciki har da umarnin kotun ƙoli na mayar da batun zuwa kotun tarayya, sun jefa makomar ‘yan siyasar cikin rashin tabbas a jam’iyyar.
Yayin da duka biyun suka tabbatar da tattaunawa da NDC, Obi ya riga ya bayyana cewa ya fice daga ADC, yayin da Kwankwaso ya buƙaci magoya bayansa su jira domin jin matakin da zai ɗauka nan gaba kaɗan.















Discussion about this post