ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, July 18, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bukatar A Kawo Karshen Cunkoso A Gidajen Gyaran Hali A Nijeriya

by Leadership Hausa
5 months ago
Cunkoso

Bisa wasu alkaluma da Hukumar Kiddiiga ta Kasa wato NBS ta fitar, sun tabbatar da cewa, duk wanda ya kai ziyara a gidajen gidan gyaran hali na kasar nan, abinda zai fara tozali da shi, shi ne, irin tsabagen matsalar cunkoson da ake fusaknata, a gidajen.

Wannan ya saba matuka, kan yadda a gina gidajen da kuma yawan adadin masu zaman Jarun, da aka kayyade, za a garkame a cikin gidajen.

  • GDPn Nijeriya Ya Yi Ƙasa Fiye da Na Shekaru 20 da Suka Wuce A Zamanin Obasanjo — Hashim
  • Sinawa Masu Amfani Da Yanar Gizo Sun Kai Biliyan 1.125

A cewar, rahoton NBS kan kididdigr Hukumar Kula da Gidajen Gidan Hali ta kasa, jmilar masu zaman gidajen, ya karu daga 69,946 a 2017, zuwa 81,710, zango na biyu na 2025.

ADVERTISEMENT

Wadannan alkaluman, sun nuna sun kai, kaso 16.82, inda karuwar ta kai ta sama da shekaru takwas da suka wuce, wanda hakan ya nuna cewa, tsarin, na kula da gidajen, ya kara lalacewa.

Sai dai, a yanzu, yawan wannan adadin a yanzu, ya zarce wanda ake da shi, a yanzu.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Gano Ma’adanin ‘Lithium’ Zai Sauya Rayuwar Al’ummar Kudancin Kaduna

Sabon Tsarin Tikitin Abinci Na Nusuk Zai Iya Ƙara Kuɗin Bizar Umrah

Kazalika, kalubalen na cunkson ne, ya haifar da tabarwarewar gidajen, inda gidajen, suka koma tamkar, wani waje, na ajiya mutane da ba a yanke masu hukunci ba.

Misali, gidan gyarn hali na jihar Legas na dauke da masu zaman Jarun guda 9,209 wanda a bisa ka’ida, an tsara za a iya ajiye, masu zaman Jarun guda 4,167 ne kawai.

Wannan ya nuna cunkoson, ya kai kaso of 221 wanda hakan, ya rubanya har sau biyu, na adadin masu zaman gidan da ya kamata a ajiye.

Jihar Ogun kuma na da masu zaman gidan gyran halin da suka kai 4,939, Kano na da 4,667, inda Enugu kuma, ke da 3,536.

Hakan ya nuna cewa, wadannan gidajen, sun tashi da sunan gidajen gyran hali, amma sun koma tamkar, wajen ajiye dabbobi, saboda rashin samun kulawa da masu zama a gidajen da kuma rashin dakunan kwana.

Batun aikin kara gina wasu gidajen daga 53,752 zuwa 65,035 aka yi niyyar yi yin aikin a 2017 zuwa 2025, batun ya kasance, kawai, rubutu ne a kan takarda, da a wamzar da shi ba, inda hakan ya nuna karuwar, ta karu zuwa kaso 20.99.

Ya sama wajibi, hukumomi su jajirce, wajen magance wannan kalubalen, musamman ta hanyar kara gina wasu sabbin gidajen.

Daga cikin wannan alkaluman na masu zaman Jarun din guda 81,710 guda 53,790, suna zaman jirin a yanke masu hukunci ne.

Bugu da kari, wannan adadain, ya karu daga 47,610 a 2017, inda karuwar kai kaso 12.98.

Wannan adadin dai, matukar abin damuwa ce, ga dukkan wani mai tunani, musamman duba da cewa, sama da kaso .65 na ‘yan Jarun din, sun kasance wadanda ba a same su, da aikata wani laifi ba.

Hakan ya nuna cewa, ba wai ana tafiyar da gidan gyran hali bane, waje ne kawai na da ake fama da talauci.

Bisa alkaluman da NBS ta fitar a 2024, an samu karin  tabarbarewar tsarin kan  yawan masu zaman gidan da ya kamata a ajiye.

Misali, a 2026, daga jimlar yawan masu zaman gidajen, sun kai  guda 176,536 94,614 da ke zaman jiran a yanke masu hukunci.

Wadanda suka aikata sata sun kai su 55,722, inda wannan adadin, ya nuna shi ne, yafi yawa daga cikin wannaan laifukan, da aka aikata.

Laifin fashi da makamai, ya kai yawan 10,090, laifun cin hanci da rashawa, sun kai guda 27, da laifin masu aikata laifun kutse a yanar gizo, inda laifun fasakauri, suka kai  118.

Idan har kasar, ba ta tashi tsaye wajen magance cin hanci da rashawa a tsakanin wasu manyan kasar ba, to bangaren na shari’a zai ci gaba da kamawa da kuma hukunta wasu marasa karfi, da ke yin sata, domin abinda za su ci.

Misali, mutumin da ya saci wayar tafi da gidanka, shi ma an sanya shi a cikin jeren masu lafi guda 55,722.

Amma dan siyasar da ya yi sama da fadi da miliyoyin kudaden da aka tsara domin gina Asibitoci da Makarantu, an sanya su jeren masu laifin cin hanci su guda 27.

Hakan dai, na ci gaba da kara rashin yardar da ‘yan kasar ke da ita, daga banragen doka da oda.

Hakazalika, adadin masu zaman gidajen su 53,790 d ba a yanke wa hukunci ba, na ci gaba da jin jiki, saboda yadda tsarin, ya gaza daidaita komai.

Wasu da daga cikinsu da dama, sun shafe shekaru, sun a zaman jiran a yanke masu hukunci, amma kotuna, na ci gaba da daga sauraron kararsu, saboda kawai, wani ra’ayi, na kashin kai, inda ko dai, dansanda mai gabatar da kara, yaki halartar zaman kotun, ko kuma ayiwa Alkali canjin wajen aiki, ko kuma kudin karar, ya bace.

Kazalika, akwai kuma wasu da suka gaza cika sharuddan samun bayar da su, beli, inda wasun da yawa kuma, ba su masaniyar hakikain laifin da suka aikata.

A bangare daya kuma, lauyoyi masu tsayawa wadanda ayyuka sun yi masu dimbin yawa.

Mu a wannan Jaridar, abinda Nijeriya ke bukata, ya wuce batun gina gidajen gyran hali.

Bugu da kari, abinda kasar ke bukata shi ne, yanke hukunci kan lokaci da kuma bayar da beli.

Matukar ba a kawo karshen wannan kalubalen ba, matsalar za ta kawai, ci gaba da karuwa ne, a kasar.

Cunkoso
Leadership Hausa
Website |  + postsBio
  • Leadership Hausa
    Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare
  • Leadership Hausa
    Tallafa Wa Yara Masu Buƙatu Na Musamman Shi Ne Burina
  • Leadership Hausa
    Dole Mata Su Rungumi Sana’o’i Domin Tsira Daga Takaicin Zamani —Ramatu Bello
  • Leadership Hausa
    Batun Dakile Shan Taba Sigari A Tsakanin Yara A Nijeriya

MASU ALAKA

Yadda Gano Ma’adanin ‘Lithium’ Zai Sauya Rayuwar Al’ummar Kudancin Kaduna
Rahotonni

Yadda Gano Ma’adanin ‘Lithium’ Zai Sauya Rayuwar Al’ummar Kudancin Kaduna

July 18, 2026
Sabon Tsarin Tikitin Abinci Na Nusuk Zai Iya Ƙara Kuɗin Bizar Umrah
Manyan Labarai

Sabon Tsarin Tikitin Abinci Na Nusuk Zai Iya Ƙara Kuɗin Bizar Umrah

July 18, 2026
Gasar Kofin Duniya: Da Ƙarfinmu Muka Kawo Matakin Da Muke Yanzu – Messi
Manyan Labarai

Gasar Kofin Duniya: Da Ƙarfinmu Muka Kawo Matakin Da Muke Yanzu – Messi

July 17, 2026
Next Post
Bunkasa Arewa Maso Yamma: Rashin Halartar Gwamnoni Ya Dusashe Armashin Taron

Bunkasa Arewa Maso Yamma: Rashin Halartar Gwamnoni Ya Dusashe Armashin Taron

LABARAI MASU NASABA

Majalisa Ta Goyi Bayan CBN Kan Sauya Fasalin Naira Bayan Tafka Muhawara 

Majalisa Ta Yi Watsi Da Bukatar MDD Ta Bincikar Badakalar Satar Daliban Oyo

July 18, 2026
Yadda Gano Ma’adanin ‘Lithium’ Zai Sauya Rayuwar Al’ummar Kudancin Kaduna

Yadda Gano Ma’adanin ‘Lithium’ Zai Sauya Rayuwar Al’ummar Kudancin Kaduna

July 18, 2026
Direbobi 123 A Kano Suna Fuskantar Tuhuma Kan Laifin Keta Dokokin Amfani Da Lambar Mota

Direbobi 123 A Kano Suna Fuskantar Tuhuma Kan Laifin Keta Dokokin Amfani Da Lambar Mota

July 18, 2026
An Kama Matashi A Kano Kan Zargin Kashe Abokinsa

‘Yansanda Sun Kama Mutum Biyu Kan Zargin Damfarar Wayar Salula A Jihar Adamawa

July 18, 2026
Sabon Tsarin Tikitin Abinci Na Nusuk Zai Iya Ƙara Kuɗin Bizar Umrah

Sabon Tsarin Tikitin Abinci Na Nusuk Zai Iya Ƙara Kuɗin Bizar Umrah

July 18, 2026
Tasirin Da VAR Ta Yi A Gasar Kofin Duniya

Tasirin Da VAR Ta Yi A Gasar Kofin Duniya

July 18, 2026
Dalilin Da Ya Sa Aka Horar Da Manoman Tumatir 100 A Garin Zariya

Dalilin Da Ya Sa Aka Horar Da Manoman Tumatir 100 A Garin Zariya

July 18, 2026
Sin Za Ta Inganta Kaddamar Da Aikin Kungiyar Hadin Gwiwar AI Ta Duniya Da Wuri

Sin Za Ta Inganta Kaddamar Da Aikin Kungiyar Hadin Gwiwar AI Ta Duniya Da Wuri

July 17, 2026
Tinubu Da Atiku Da Obi Na Ci Gaba Da Zafafa Neman Kuri’un Arewacin Nijeriya

Tinubu Da Atiku Da Obi Na Ci Gaba Da Zafafa Neman Kuri’un Arewacin Nijeriya

July 17, 2026
Sin Ta Yaba Da Matakin Amurka Na Kin Tsawaita Dokar Ta-Baci Dangane Da HK

Sin Ta Yaba Da Matakin Amurka Na Kin Tsawaita Dokar Ta-Baci Dangane Da HK

July 17, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.