ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, July 19, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zaben Fidda Gwani: Gwamna Dauda Ya Ayyana Ighodalo A Matsayin Ɗan Takardar PDP A Zaɓen Jihar Edo

by Leadership Hausa
2 years ago
gwamna

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal ya jagoranci zaɓen fitar da gwani na Jam’iyyar PDP a zaɓen Gwamnan jihar Edo da ke tafe.

A zaɓen da ya gudana yau Alhamis a filin wasa na Samuel Ogbemudia da ke garin Benin, Asue Ighodalo ne ya zama zakara, wanda ke nuni da cewa shi ne zai yi wa jam’iyyar takara a Edo.

A wata sanarwa da mai magana da yawun Gwamnan, Sulaiman Bala Idris ya fitar a Abuja, ya bayyana cewa zaɓen ya gudana cikin tsari da kwanciyar hankali, inda aka zaɓi wanda zai yi wa jam’iyyar PDP takara a zaɓen Gwamnan da ke tafe cikin watan Satumba mai zuwa.

ADVERTISEMENT
  • Hukumar Kwastom Ta Fara Sayarwa ‘Yan Nijeriya Kayan Abincin Da Ta Kwace A Legas

 

Tun farko a jawabin sa kafin a fara zaɓen, Gwamna Dauda Lawal ya hori ‘yan takarar da su yi amanna da tsarin zaɓen, inda ya ba su tabbacin za a gudanar da zaɓe mai cike da adalci.

LABARAI MASU NASABA

Majalisa Ta Yi Watsi Da Bukatar MDD Ta Bincikar Badakalar Satar Daliban Oyo

Yadda Gano Ma’adanin ‘Lithium’ Zai Sauya Rayuwar Al’ummar Kudancin Kaduna

“Ko yanzu za ku iya gani, an yi tsari mai kyau buɗaɗɗe. Za mu gudanar da zaɓe na gaskiya mai inganci don samar da ɗan takara ga jam’iyyar mu a jihar Edo.”

Sanarwar ta Malam Idris ta ce, bayan kammala zaɓe da ƙirgawa, Gwamna Dauda Lawal, a matsayinsa na Baturen zaɓe, ya bayyana Ighodalo a matsayin gwanin da aka fitar bayan ya samu ƙuri’u 577, wanda ya doke sauran ‘yan takarar su tara.

“A matsayina na jagoran gudanar da zaɓen fitar da gwani na jam’iyyar PDP, na bayyana Asuelimen Ighodalo a matsayin wanda ya lashe zaɓen da kuri’u 577.

“Ina taya shi murna, tare da yin kira ga sauran ‘yan takarar da su karɓi wannan sakamako da zuciya ɗaya. Wajibin mu ne mu haɗa kai mu dumfari yaƙi na gaba, zaɓen Gwamna.

“Wajibin mu ne mu sanya buƙatun jam’iyya birbishin buƙatunmu. Yanzu muna da ɗan takara, dolen mu mu bayar da cikakken goyon bayanmu,” In ji Gwamna Dauda.

gwamna
Leadership Hausa
Website |  + postsBio
  • Leadership Hausa
    Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare
  • Leadership Hausa
    Tallafa Wa Yara Masu Buƙatu Na Musamman Shi Ne Burina
  • Leadership Hausa
    Dole Mata Su Rungumi Sana’o’i Domin Tsira Daga Takaicin Zamani —Ramatu Bello
  • Leadership Hausa
    Batun Dakile Shan Taba Sigari A Tsakanin Yara A Nijeriya

MASU ALAKA

Majalisa Ta Goyi Bayan CBN Kan Sauya Fasalin Naira Bayan Tafka Muhawara 
Labarai

Majalisa Ta Yi Watsi Da Bukatar MDD Ta Bincikar Badakalar Satar Daliban Oyo

July 18, 2026
Yadda Gano Ma’adanin ‘Lithium’ Zai Sauya Rayuwar Al’ummar Kudancin Kaduna
Rahotonni

Yadda Gano Ma’adanin ‘Lithium’ Zai Sauya Rayuwar Al’ummar Kudancin Kaduna

July 18, 2026
Direbobi 123 A Kano Suna Fuskantar Tuhuma Kan Laifin Keta Dokokin Amfani Da Lambar Mota
Kotu Da Ɗansanda

Direbobi 123 A Kano Suna Fuskantar Tuhuma Kan Laifin Keta Dokokin Amfani Da Lambar Mota

July 18, 2026
Next Post
Sake Dawowar Matsalar Tsaro

A Tona Asirin Kungiyoyin Addinin Da Ke Daukar Nauyin Ta’addanci

LABARAI MASU NASABA

An Kaddamar Da “Bikin Fasahar AI Na Sin Na 2026” A Shanghai

An Kaddamar Da “Bikin Fasahar AI Na Sin Na 2026” A Shanghai

July 18, 2026
Fim Ko Gaske:Yaushe Masu Kallon Fina-finai Za Su Daina Daukar Fim A Matsayin Gaske

Fim Ko Gaske:Yaushe Masu Kallon Fina-finai Za Su Daina Daukar Fim A Matsayin Gaske

July 18, 2026
Sin Ta Nuna Matukar Adawa Da Matakin Burtaniya Na Mallake Kamfanin Karafa Na British Steel

Sin Ta Nuna Matukar Adawa Da Matakin Burtaniya Na Mallake Kamfanin Karafa Na British Steel

July 18, 2026
Tasirin AI (Artificial Intelligence) A Harkokin Al’umma Na Yau Da Kullum

Tasirin AI (Artificial Intelligence) A Harkokin Al’umma Na Yau Da Kullum

July 18, 2026
Xavi Ya Ce A Shirye Yake Ya Karɓi Ragamar Horar Da Tawagar Ƙasa

Xavi Ya Ce A Shirye Yake Ya Karɓi Ragamar Horar Da Tawagar Ƙasa

July 18, 2026
Masanin Kimiyya Na Sin Ya Lashe Kyautar UNESCO-Russia Mendeleev A Fannin Tushen Kimiyya

Masanin Kimiyya Na Sin Ya Lashe Kyautar UNESCO-Russia Mendeleev A Fannin Tushen Kimiyya

July 18, 2026
Burina Zama Daya Daga Cikin Fitattun Masu Daukar Hoto A Nijeriya –Ibrahim Aminu

Burina Zama Daya Daga Cikin Fitattun Masu Daukar Hoto A Nijeriya –Ibrahim Aminu

July 18, 2026
Omar M. Yaghi: Kalaman Xi Sun Kara Mana Kwarin Gwiwa

Omar M. Yaghi: Kalaman Xi Sun Kara Mana Kwarin Gwiwa

July 18, 2026
Manufar Sin Ta Ba Da Jagoranci Ga Tafiyar Da Fasahar AI A Duniya

Manufar Sin Ta Ba Da Jagoranci Ga Tafiyar Da Fasahar AI A Duniya

July 18, 2026
CDC Ta Afirka Ta Yaba Wa Sin Bisa Goyon Bayanta Ga Dakile Cutar Ebola

CDC Ta Afirka Ta Yaba Wa Sin Bisa Goyon Bayanta Ga Dakile Cutar Ebola

July 18, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.