Hukumar gudanarwar Jami’ar Tarayya ta Ilimi (FUE), Pankshin, a Filato, ta gano wasu mutane da suka ƙware wajen ƙirƙira da sauya sakamakon karatu da takardun shaidar kammala karatu na jami’ar. Muƙaddashin Shugaban Jami’ar, Farfesa Jere Ndazhaga, ne ya bayyana hakan yayin ganawa da ƴan jarida a Jos.
A cewarsa, an gano wannan mummunan aiki ne bayan wani mutum ya miƙa shaidar karatu mai cike da shakku a sashin jarrabawa da rijista na jami’ar, yana ƙorafin cewa ba a ɗora sakamakonsa a tsarin JAMB ba. Hangen nesa da ƙwarewar ma’aikatan da ke bakin aiki ne suka sa aka gano saɓanin bayanai, a cikinsa, lamarin da ya jawo sanar da sashin tsaron jami’ar tare da tuntuɓar ƴansanda a Pankshin.
Binciken sirri na jami’an tsaro ya kai ga cafke Friday Tunkyes daga ƙaramar hukumar Mikang, sannan daga bisani aka kama Harvey Obed Ringsum daga Mangu. A yayin sumamen, an ƙwato takardun shaidar karatu na bogi masu yawa da hatimin jami’ar, lamarin da ya tabbatar da wanzuwar gungun masu damfarar. Daga ƙarshe, kotu ta same su da laifi tare da yanke musu hukuncin ɗaurin shekara ɗaya da rabi kowannensu.
Farfesa Ndazhaga ya ce jami’ar ba za ta lamunci duk wani aiki da zai ɓata martabarta ko rage darajar ilimi ba, tare da kira ga hukumomi da ma’aikata su riƙa tantance sahihancin takardun karatu. Ya ƙara da cewa jami’ar na da aniyar zama cibiyar ilimi mai inganci, kuma ta buƙaci jama’a da su riƙa kai rahoton duk wani abu da ke barazana ga mutuncin ilimi.














