ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ko Kin San… Sirrikan Nuna Soyayya Ga Miji?

by Bilkisu Tijjani and Sulaiman
2 years ago
Soyayya

Assalamu alaikum masu karatu, barkan mu da sake haduwa daku a wannan makon a cikin shirin na mu mai farin jini da albarka na Ko Kin San.

A yau shafin na mu zai yi magana ne akan yadda wasu mata suka dauki kansu da cewa wai su sun girmi yin soyayya.

 

ADVERTISEMENT

Wai sun girma ba a soyayya:

Yanzu dai bari na fara da ke uwargida: Ya kamata ki saurari duk nasihohin da zan miki, ki gode wa Allah wurin yin amfani da baiwar da ya yi miki, na kasancewa uwargida, wato komai dai yana hannunki ne har da shi kansa maigidan naki, a daidai wannan gabar in ka ji mace tana kukan yadda sitiyarin maigidan ya yi karfi, har ta kai ga cewa ba ta iya juyawa, to ta binciki kanta.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Ake Kula Da Labba Domin Su Kasance Masu Laushi

Yadda Ake Kare Hannu Daga Bushewa

 

Hakika Allah S.W.T yana cewa:

“An kawata wa mutane son ababan sha’awa daga mata”.

Asali ke abar sha’awa ce ko kin yi ado ko ba ki yi ba, to me zai sa ba za ki yi adon domin ki karkato da hankalin maigidanki zuwa gare ki ba. Wasu matan su kan kalli wasan kwaikwayon Indiya sai su rika sha’awar yadda maza suke ma’amalla da matansu, wasu kuma wasu kuma wasan kwaikwayon Hausa suke kallo, to amma akwai wani abin lura, shi ne, shin mu a wannan matattarar tamu, mace ta kan kure adaka ta sha turare ga lalle yana daukar hankali, ta saka kayan da za su rika fizgar hankalin mai kallo don kawai ta yi rawa a gaban maigidanta ta tayar masa da sha’awarsa ya ji yana bukatarta.

Mai yuwuwa wani ya ce wannan al’adar Yahudu da Nasara ce, ko ita matar malam Bahaushe ta ce haba wannan ai sai yara mu mun girma ko ta ce sai kuma a ganki tsofai-tsofai da ke ga yara sun isa aure kina yi wa maigida rawa to amma kuma tana bukatar soyayyarsa.

Asshaikh Nasiruddeen Al’Albani RH ya fitar da wata fatawa a cikin majallar (Mujallatul Asaalah 8/ 74) yake cewa rawar da mace za ta yi a gaban maigidanta rawa kawai da aka saba ba wai na gaban jama’a ba (ba wai a wasan kwaikwayo da wuraren bukukuwa ba), kuma ba koyo ta yi masamman don ta rika yi ana gani ba, wannan ko da za ta motsa sha’awar maigida babu wani nassi da ya haramta, amma da sharadin cewa daga ita sai maigidanta kawai.

An tambayi malam cewa:

To in ta saka irin kayan da masu rawa a wasannin kwaikwayo suke sakawa tsaya a gaban mijinta, ashe wannan ba koyi da su take yi ba, kuma da nuna kauna ga abin da suke yi, sai ya ce “Wannan halas ne matukar a tsakankanin ma’auratan ne, kuma ba wani ba.

Soyayya
Bilkisu Tijjani
+ posts Bio
  • Bilkisu Tijjani
    https://hausa.leadership.ng/author/bilkisu-tijjani/
    Tuwon Alkama Da Miyar Taushe
  • Bilkisu Tijjani
    https://hausa.leadership.ng/author/bilkisu-tijjani/
    Yadda Ake Kula Da Labba Domin Su Kasance Masu Laushi
  • Bilkisu Tijjani
    https://hausa.leadership.ng/author/bilkisu-tijjani/
    Yadda Ake Chicken Teriyaki Rice
  • Bilkisu Tijjani
    https://hausa.leadership.ng/author/bilkisu-tijjani/
    Yadda Ake Kare Hannu Daga Bushewa
Soyayya
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan
  • Sulaiman
    ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto
  • Sulaiman
    PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi
  • Sulaiman
    Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

MASU ALAKA

Yadda Ake Kula Da Labba Domin Su Kasance Masu Laushi
Ado Da Kwalliya

Yadda Ake Kula Da Labba Domin Su Kasance Masu Laushi

September 5, 2026
Yadda Ake Kare Hannu Daga Bushewa
Ado Da Kwalliya

Yadda Ake Kare Hannu Daga Bushewa

August 29, 2026
Soyayya
Ado Da Kwalliya

Yadda Ake Kula Da Farce

August 23, 2026
Next Post
Mashawarcin Shugaban Amurka Kan Harkokin Tsaro Jake Sullivan Zai Ziyarci Kasar Sin 

Mashawarcin Shugaban Amurka Kan Harkokin Tsaro Jake Sullivan Zai Ziyarci Kasar Sin 

LABARAI MASU NASABA

Iran Ta Musanta Ikirarin Trump Tare Da Zafafa Hare-hare Kan Isra’ila

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

September 9, 2026
ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.