Majalisar Dokokin Jihar Kano ta tabbatar da karɓar wasiƙar Gwamna Abba Kabir Yusuf wadda ke neman tantance Murtala Sule Garo a matsayin mataimakin gwamna. Kakakin majalisar, Jibrin Ismaila Falgore, ne ya sanar da hakan bayan karanta wasiƙar a zaman majalisa ranar Laraba.
Wannan na zuwa ne bayan naɗin da gwamnan ya yi wa Garo domin cike gurbin da ya samu sakamakon murabus ɗin Comrade Aminu Abdussalam Gwarzo a watan da ya gabata. A cikin wasiƙar, gwamnan ya bayyana halayen kirki, da kwarewa da gogewar Garo, tare da irin gudunmawar da ya bayar ga jam’iyyar APC da kuma ci gaban jihar Kano.
Naɗin ya yi daidai da sashi na 191(3) na Kundin Tsarin Mulki na 1999 (wanda aka gyara), wanda ke bai wa gwamna damar naɗa mataimaki idan gurbi ya samu. Bayan karanta wasiƙar, kakakin majalisar ya sanar da kafa kwamitin wucin gadi domin tantance wanda aka naɗa.
Kwamitin, ƙarƙashin jagorancin mataimakin kakakin majalisa, ya kunshi manyan shugabannin majalisa da wakilan mazaɓu daban-daban, kuma ana sa ran zai gayyaci Garo domin tantancewa tare da miƙa rahotonsa ga majalisar ranar Litinin.
Garo mai shekaru 48 ya riƙe mukamai da dama a baya, ciki har da shugaban ƙaramar hukuma, da shugaban ALGON Kano, da kwamishina da kuma ɗan takarar mataimakin gwamna na APC a zaɓen 2023.















Discussion about this post