ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shettima Ya Isa Switzerland Don Jagorantar Tawagar Nijeriya A Taron Tattalin Arziƙin Duniya

by Abubakar Sulaiman
8 months ago
Shettima

Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima, ya isa garin Davos da ke Switzerland domin jagorantar tawagar Nijeriya a taron shekara-shekara na 56 na Hukumar Tattalin Arziƙin Duniya (WEF), wanda za a gudanar daga ranar 19 zuwa 23 ga Janairu, 2026. A cewar sanarwar mai magana da yawunsa, Stanley Nkwocha, Shettima ya iso ne daga Conakry ta Guinea, inda ya wakilci Shugaba Bola Tinubu a bikin rantsar da Shugaban Ƙasar Guinea, Mamadi Doumbouya, a ranar Asabar.

A isarsa, Ministan Harkokin Waje, Ambasada Yussuf Tuggar, da Ministan Kasuwanci da Zuba Jari, Dakta Jumoke Oduwole, tare da jami’an ofishin jakadancin Nijeriya a Switzerland, suka tarɓe shi. Ziyarar ta zo ne a daidai lokacin da Nijeriya ke ƙara ƙaimi wajen faɗaɗa hulɗar tattalin arziki da ƙasashen duniya da manyan masu zuba jari.

  • Shettima Ya Ce Zuba Jari A Ɓangaren  Ilimi Ba Caca Ba Ce
  • Tinubu Na Ɗaukar Ƙwararan Matakai Don Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya – Shettima

Taron WEF na shekarar 2026 ya zama muhimmin tarihi ga Nijeriya, inda karo na farko gwamnatin tarayya ta ƙaddamar da “Nigeria House Davos” — wata cibiya ta musamman a titin Davos Promenade. Wannan cibiyar, wadda aka samar ta hanyar haɗin gwuiwar gwamnati da kamfanoni masu zaman kansu (PPP), za ta zama dandalin tattaunawa da ministoci, da tarukan masu zuba jari, da kuma hulɗar al’adu a tsawon makon taron.

ADVERTISEMENT

A yayin taron, Shettima zai gabatar da hangen nesa na tattalin arziƙin Nijeriya na 2026 ga manyan shugabannin siyasa da ƴan kasuwa na duniya, tare da halartar zaman tattaunawa kan amfani da fasahar sadarwa ta ƙirƙirarriyar basira (AI), da quantum computing da kimiyyar halittu.

Har ila yau, zai gana da shugabannin ƙasashe, da manyan kamfanoni da cibiyoyin kuɗaɗen ci gaba domin ƙarfafa haɗin gwuiwa da ya yi daidai da Ajandar “Renewed Hope” ta Shugaba Bola Ahmed Tinubu. Minista Jumoke Oduwole ta ce Nijeriya za ta gabatar da damammakin zuba jari a fannoni kamar ma’adinai, da noma mai ɗorewa, da ƙirƙira da fasahar dijital ga masu zuba jari daga sassa daban-daban na duniya.

LABARAI MASU NASABA

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

Shettima
Abubakar Sulaiman
Website |  + postsBio
  • Abubakar Sulaiman
    Iyalin El-Rufai Sun Bai Ministan Tsaro Wa’adin Kwana 7 Kan Zargin Rikicin Kudancin Kaduna
  • Abubakar Sulaiman
    Atiku Ya Zargi Gwamnatin Tarayya Da Cin Bashi Kamar Mashayin Da Kuɗi Ya Ƙarewa
  • Abubakar Sulaiman
    Boko Haram Ta Kai Hari Adamawa, Ana Fargabar Mutuwar Mutane 11
  • Abubakar Sulaiman
    Ƴan Bindiga Sun Kai Hari Sokoto, Sun Kashe Mutane 7, Sun Yi Garkuwa Da 12

MASU ALAKA

Iran Ta Musanta Ikirarin Trump Tare Da Zafafa Hare-hare Kan Isra’ila
Manyan Labarai

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

September 9, 2026
Sojoji
Manyan Labarai

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Ballon D'or
Manyan Labarai

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

September 8, 2026
Next Post
Shin Alonso Ya Cancanci Kora A Real Madrid?

Rashin Tsaro A Nijeriya: Gazawar Masu Mulki Ce Da Cin Amanar Ƙasa

LABARAI MASU NASABA

Iran Ta Musanta Ikirarin Trump Tare Da Zafafa Hare-hare Kan Isra’ila

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

September 9, 2026
ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.