ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, July 19, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tashar Jiragen Ruwa Ta Lekki Ta Fara Tarbar Kwantaina Daga Kasashen Afirka

by Leadership Hausa
7 months ago
lekki

Daga Abubakar Abba

Tasahar Jiragen Ruwa ta Lekki da ke a Jihar Legas, ta fara tarbar manyan kayan da aka yo jigilarsu daga yankunan Tashoshin Jiragen Ruwa na wasu kasashen da ke Afirka, inda ta fara tarbar Kwantainoni kaso 20, da aka yo jigilaru a 2025.

Jaridar BusinessDay ta ruwaito cewa, hakan ya zama wata babbar nasara ta farko ga kasar nan, tun bayan fara gudanar da tura ababen hawa daga Tashar TinCan island a 2024. Zuwa kasar China.

  • Shari’ar Annabi SAW Ta Fi Ta Sauran Annabawa Sauƙi
  • Buƙatar A Sake Duba Sabuwar Dokar Haraji

A cewar wasu alkaluman da aka fitar a hukumance, a yanzu wajen ajiya kayan da aka yo jigilarsu a Tasahar, sun kai kimanin kaso 50 daga kaso 20, a watan Yulin 2025.

ADVERTISEMENT

Babban Jami’in da ke kula da ke sanya ido a wajen da akae ajiya kaya a Tasahar ta Lekki Ajay Tyagi, ya bayyana cewa, a yanzu haka ana sauke Kwantainoni da dama a wajen aje kayan na Tashar wadanda kuma ake tura su zuwa Tashar Jiragen Ruwa ta Tema, da ke a kasar Côte d’Iboire.

Tyagi ya sanar da cewa, Tashar ta Lekki, na ci gaba da samun karuwar shigo da Kwantainoni kafin kaisu, zuwa wasu kasuwannin da ke makwabtaka da da sauran kasashe.

LABARAI MASU NASABA

Dalilin Da Ya Sa Kungiyar NCTR Ta Jinjina Wa Shugaban NPA

Ɗantsoho Ya Jinjina Wa Hukumar FCC Kan Sabbin Sauye-Sauyen Da Ta Samar

Shi kuwa Manajan Darakta da ke kula da wajen aje kayan a Tashar ta Lekki Jedrzej Mierzewski, ya sanar da cewa, kasuwar ta cikin kasar nan na kara bayar da wata damar wajen janyo ra’ayin masu shigo da kaya ta ruwa, zuwa cikin kasar nan.

Ya kara da cewa, hakan na kuma kara samar da sauki wajen shigo da kaya ta hanyar ruwa, zuwa cikin kasar.

Mierzewski ya kuma yi gargadi da cewa, tura kayan ya danganta ne, bisa yin hadin guiwa a tsakanin masu tafiyar da wguraren da ake ajiye kayan da aka shigo da su da masu sanya ido da kuma abokan hudda.

“Muna bukatar mu rinka yin aiki kafada da kafada da sauran masu ruwa da tsaki da ke a fannin na sufurin Jiragen Ruwa, kuma zamu iya samar da farashin da za a iya yin gasa akansa wanda ya yi daidai da tsarin sufurin Jiragen Ruwa na kasar nan, “Inji shi.

Ya yi nuni da cewa, yanayin kwarewar da aka samu daga kasar Poland ta shekaru da dama, wani misali ne kan yadda hakan ya samar da sabon babin gudanar da gasa a Tashar Jiragen Ruwan.

A cewarsa, a wancan lokacin daga Tashar Jiragen Ruwan ta kasar ta Poland, ana tura kaya zuwa Tashoshin Jiragen Ruwa na kasar Jamus

A cewar mahukuntan Tashar ta Lekki, a yanzu haka ana sauke mayan motoci kimanin 200 da suka yo jigilar kaya zuwa Tashar, wanda hakan ke ci gaba da faruwa, saboda samar da na’urar zamani da a turance, ake kira da electronic call-up system wacce ke kara ingnata ayyukan da ake gudanarwa a Tashar.

Kazalika, mahukuntan Tashar sun bayyana cewa, kara fadada aikin Tashar ta Lekki, ya dogara ne kawai kan kara samun gudanar da ayyuka tare da kara samar da kayan aiki a daukacin tsarin na hada-hadar sufurin Jiragen Ruwa.

Leadership Hausa
Website |  + postsBio
  • Leadership Hausa
    Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare
  • Leadership Hausa
    Tallafa Wa Yara Masu Buƙatu Na Musamman Shi Ne Burina
  • Leadership Hausa
    Dole Mata Su Rungumi Sana’o’i Domin Tsira Daga Takaicin Zamani —Ramatu Bello
  • Leadership Hausa
    Batun Dakile Shan Taba Sigari A Tsakanin Yara A Nijeriya

MASU ALAKA

NPA Ta Tara Kudin Shiga Naira Biliyan 758.2 A 2024
Tattalin Arziki

Dalilin Da Ya Sa Kungiyar NCTR Ta Jinjina Wa Shugaban NPA

July 17, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Tattalin Arziki

Ɗantsoho Ya Jinjina Wa Hukumar FCC Kan Sabbin Sauye-Sauyen Da Ta Samar

July 11, 2026
NNPCL Ya Rage Farashin Man Fetur Zuwa ₦860 Kan Kowacce Lita – IPMAN
Tattalin Arziki

Rage Farashin Mai Na Ɗangote: Dillalan Man Fetur Sun Yi Burus Da Sauya Nasu Farashin

June 27, 2026
Next Post
Gwamna Abba Ya Kammala Shirye-shiryen Komawa APC A Ranar Litinin

Gwamna Abba Ya Kammala Shirye-shiryen Komawa APC A Ranar Litinin

LABARAI MASU NASABA

An Kaddamar Da “Bikin Fasahar AI Na Sin Na 2026” A Shanghai

An Kaddamar Da “Bikin Fasahar AI Na Sin Na 2026” A Shanghai

July 18, 2026
Fim Ko Gaske:Yaushe Masu Kallon Fina-finai Za Su Daina Daukar Fim A Matsayin Gaske

Fim Ko Gaske:Yaushe Masu Kallon Fina-finai Za Su Daina Daukar Fim A Matsayin Gaske

July 18, 2026
Sin Ta Nuna Matukar Adawa Da Matakin Burtaniya Na Mallake Kamfanin Karafa Na British Steel

Sin Ta Nuna Matukar Adawa Da Matakin Burtaniya Na Mallake Kamfanin Karafa Na British Steel

July 18, 2026
Tasirin AI (Artificial Intelligence) A Harkokin Al’umma Na Yau Da Kullum

Tasirin AI (Artificial Intelligence) A Harkokin Al’umma Na Yau Da Kullum

July 18, 2026
Xavi Ya Ce A Shirye Yake Ya Karɓi Ragamar Horar Da Tawagar Ƙasa

Xavi Ya Ce A Shirye Yake Ya Karɓi Ragamar Horar Da Tawagar Ƙasa

July 18, 2026
Masanin Kimiyya Na Sin Ya Lashe Kyautar UNESCO-Russia Mendeleev A Fannin Tushen Kimiyya

Masanin Kimiyya Na Sin Ya Lashe Kyautar UNESCO-Russia Mendeleev A Fannin Tushen Kimiyya

July 18, 2026
Burina Zama Daya Daga Cikin Fitattun Masu Daukar Hoto A Nijeriya –Ibrahim Aminu

Burina Zama Daya Daga Cikin Fitattun Masu Daukar Hoto A Nijeriya –Ibrahim Aminu

July 18, 2026
Omar M. Yaghi: Kalaman Xi Sun Kara Mana Kwarin Gwiwa

Omar M. Yaghi: Kalaman Xi Sun Kara Mana Kwarin Gwiwa

July 18, 2026
Manufar Sin Ta Ba Da Jagoranci Ga Tafiyar Da Fasahar AI A Duniya

Manufar Sin Ta Ba Da Jagoranci Ga Tafiyar Da Fasahar AI A Duniya

July 18, 2026
CDC Ta Afirka Ta Yaba Wa Sin Bisa Goyon Bayanta Ga Dakile Cutar Ebola

CDC Ta Afirka Ta Yaba Wa Sin Bisa Goyon Bayanta Ga Dakile Cutar Ebola

July 18, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.