Wani matashi mai shekara 30 da ke rayuwa da nakasa, Mahmud Sadis Buba, ya samu nasarar tsallake tantancewar jam’iyyar APC gabanin zaɓen fidda gwani na kujerar majalisar wakilai ta tarayya a jihar Kaduna.
Buba, wanda aka fi sani da “Abin Al-Ajabin Zazzau,” na neman wakiltar mazabar Sabon Gari ta tarayya a ƙarƙashin APC. Matashin wanda ke da gajertar jiki ya ja hankalin jama’a a kafafen sada zumunta bayan bidiyon tantancewarsa ya bazu a yanar gizo.
Da yake jawabi yayin tantancewar, Buba ya ce mutanen mazaɓarsa ne suka ƙarfafa masa gwuiwar shiga takarar domin yi musu hidima. “Ba don kaina nake yin wannan ba. Mutane ne suka kira ni domin in yi musu aiki, kuma zan yi musu,” in ji shi.
Ya bayyana cewa shi ne babban ɗa a cikin ‘ya’ya tara kuma yana da shaidar kammala makarantar sakandare. Shigarsa takarar ya janyo yabo daga magoya baya da masu sharhi kan siyasa, inda da dama suka bayyana hakan a matsayin wata alama ta ƙaruwa da bai wa masu nakasa dama a harkokin siyasa.
Buba na neman kujerar ne daga hannun Sadiq Ango Abdullahi, wanda aka zaɓa a 2023 ƙarƙashin jam’iyyar PDP kafin daga bisani ya koma APC, kuma yanzu haka shi ma yana neman sake tsayawa takara a ƙarƙashin jam’iyyar mai mulki.















Discussion about this post