Wani ɗalibi na Jami’ar Jos, John Arum Azi, wanda aka sace kusan makonni biyu da suka gabata, ya samu ‘yanci daga hannun masu garkuwa da shi. Ya isa birnin Jos na jihar Filato a daren Laraba da misalin ƙarfe 10, bayan an sace shi a yayin tafiyarsa, lamarin da ya jawo cece-kuce bayan bidiyon azabtar da shi ya bazu a intanet.
Daga bisani an gano cewa an yi garkuwa da shi ne a Zariya, ba a kan hanyarsa ta zuwa Kaduna ba kamar yadda aka ruwaito da farko, inda ya je neman aiki kafin a kai shi cikin daji. An kuma tafi da shi daga Kaduna zuwa Zamfara, lamarin da ya haddasa jita-jitar cewa an kashe shi kafin daga bisani wani bidiyo ya nuna an sake shi.
Ɗan’uwansa, Bulus, ya bayyana cewa iyalansu sun riƙa tuntuɓar masu garkuwa da shi tun daga farko, suna tura musu kuɗaɗe na kati da wasu buƙatu yayin da ake tattaunawa kan kuɗin fansa. Ya ce an fara amincewa da Naira miliyan 6, amma daga bisani aka ƙara zuwa miliyan 15 bayan an fara tara kuɗi ta intanet, kafin daga ƙarshe aka biya Naira miliyan 10,315,000 domin samun ‘yancinsa.
Bayan biyan kuɗin, an dawo da Azi tare da wani mutum ta kan babura daga Zamfara zuwa Zariya, inda aka kai su asibiti kafin daga bisani iyalansa suka ɗauke shi zuwa Jos. A yanzu haka yana kwance a Asibitin Koyarwa na Jami’ar Jos (JUTH) yana karɓar magani, yayin da iyalansa suka ce yana da raunuka a jikinsa sakamakon dukan da ya sha a hannun masu garkuwa da shi.















Discussion about this post