ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, September 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Bindiga: ‘Yansanda Sun Ceto Mutum Uku Gami Da Kwato Bindigar AK-47 A Gombe

by Rabi'u Ali Indabawa
7 months ago
Gombe

Rundunar ‘Yansandan Jihar Gombe ta ceto mutum uku da aka sace tare da kwato bindigogi AK-47 guda biyu, bayan wani hari da ake zargin ‘yan bindiga ne suka kai a Gundumar Pindiga da ke Karamar Hukumar Akko a jihar.

A cikin wata sanarwa da rundunar ta fitar, Jami’in Hulda da Jama’a na rundunar, DSP Buhari Abdullahi, ya ce harin ya faru ne a kauyukan Rahama, Lambo da Garin Galadima.

  • An Nada Liu Xianfa Wakilin Musamman Na Gwamnatin Sin Kan Harkokin Afirka
  • Yadda Buƙatun Kwankwaso Suka Tarwatsa Yiwuwar Haɗin Gwuiwa Da APC

Sanarwar ta bayyana cewa harin ya fara ne da safiyar ranar 24 ga Janairu, 2026.

ADVERTISEMENT

“Ranar 24/01/2026 da misalin karfe 02:00 na dare, bayanan da aka samu sun nuna cewa wasu da ake zargin ‘yan bindiga sun kai hari kauyen Rahama ta hanyar Gagarabami, inda suka harbe tare da kashe Tela Bello Ahmadu, mai shekaru 70,” in ji ‘yansanda.

Sanarwar ta kara da cewa maharan daga bisani sun sace ‘ya’yansa biyu, Saleh Tela (mai shekaru 25) da Abdullahi Tela (mai shekaru 35).

LABARAI MASU NASABA

Direbobi 123 A Kano Suna Fuskantar Tuhuma Kan Laifin Keta Dokokin Amfani Da Lambar Mota

‘Yansanda Sun Kama Mutum Biyu Kan Zargin Damfarar Wayar Salula A Jihar Adamawa

Abdullahi ya ce wannan kungiya ta tafi kauyen Lambo da misalin karfe 3:40 na dare, inda suka sace wasu mazauna uku.

“Sun sace Babayo Garba, mai shekaru 30, Malam Abba Musa, mai shekaru 45, da Baayo Bayi, mai shekaru 20,” in ji shi.

Bayan karbar kiran agaji, kungiyoyin sintirin ‘yansanda karkashin Operation Hattara, tare da hadin gwiwar mafarauta da ‘yan sa-kai, sun tafi wurin suka yi arangama da maharan.

“Yayin aikin, Baayo Bayi, abin takaici, ya fada cikin musayar wuta kuma daga baya aka tabbatar da rasuwarsa, yayin da Babayo Garba da Malam Abba Musaaka ceto su lafiya,” in ji sanarwar.

‘Yansanda sun ce an kashe wasu daga cikin maharan uku yayin musayar wuta, yayin da sauran suka tsere zuwa cikin daji, inda ake zargin sun samu raunuka daga harbin bindiga.

Abubuwan da aka kwato daga aikin sun hada da: bindigogi AK-47 guda biyu, jigida guda hudu, harsasai 68 na 7.62mm, harsasai 120 da aka harba, babura guda hudu da kuma kudi Naira 2,300.

An kai wadanda aka ceto asibiti domin gwajin lafiya.

Rundunar ta ce an kara kokari wajen kama maharan da suka tsere, sannan za a sanar da al’umma da zarar an samu ci gaba.

Kwamishinan ‘Yansanda, CP Umar Ahmed Chuso, ya tabbatar wa mazauna jihar cewa rundunar na nan daram wajen tabbatar da tsaro.

“Ya tabbatar wa jama’a cewa rundunar ba za ta yi kasa a gwiwa wajen kare rayuka da dukiyoyi a fadin jihar ba, sannan ya yi kira ga jama’a da su ci gaba da ba da goyon baya ta hanyar samar da sahihan bayanai cikin lokaci ga ‘yansanda,” in ji sanarwar.

Gombe
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƙungiya Ta Gudanar Da Zaɓen Sabbin Shugabanninta A Abuja
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Jihar Katsina Da UNICEF Sun Ceto Rayuwar Yara Ta Hanyar Samar Da Abinci Mai Gina Jiki
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Yadda Tinubu Ya Kashe Naira Biliyan 37.64 A Tafiye-tafiye
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ta’addaci: Mutum 14,500 Sun Bace A Arewa Maso Gabas

MASU ALAKA

Direbobi 123 A Kano Suna Fuskantar Tuhuma Kan Laifin Keta Dokokin Amfani Da Lambar Mota
Kotu Da Ɗansanda

Direbobi 123 A Kano Suna Fuskantar Tuhuma Kan Laifin Keta Dokokin Amfani Da Lambar Mota

July 18, 2026
An Kama Matashi A Kano Kan Zargin Kashe Abokinsa
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Kama Mutum Biyu Kan Zargin Damfarar Wayar Salula A Jihar Adamawa

July 18, 2026
Disu
Kotu Da Ɗansanda

IGP Disu Ya Hana Jami’an Ƴansanda Yin Amfani Da TikTok Da Instagram Da Sauransu

June 26, 2026
Next Post
Za A Fuskanci Karancin Motoci A Nijeriya Sakamakon Karin Haraji

Wani Direba Da Ya Buge Mai PoS Har Lahira Ya Tsere A Abuja

LABARAI MASU NASABA

Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara

Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara

September 10, 2026
Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

September 10, 2026
’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya

’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya

September 10, 2026
2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

September 10, 2026
Zabe: Gwamnatin Kano Ta Taƙaita Zirga-zirgar Mutane Da Ababen Hawa

Gwamna Yusuf Ya Umarci Jami’an Tsaro Su Gano Waɗanda Suka Kashe Danshagamu

September 10, 2026
Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

September 9, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

September 9, 2026
Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

September 9, 2026
Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa

Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa

September 9, 2026
Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

September 9, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.