ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, July 14, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Bindiga: ‘Yansanda Sun Ceto Mutum Uku Gami Da Kwato Bindigar AK-47 A Gombe

by Rabi'u Ali Indabawa
5 months ago
Gombe

Rundunar ‘Yansandan Jihar Gombe ta ceto mutum uku da aka sace tare da kwato bindigogi AK-47 guda biyu, bayan wani hari da ake zargin ‘yan bindiga ne suka kai a Gundumar Pindiga da ke Karamar Hukumar Akko a jihar.

A cikin wata sanarwa da rundunar ta fitar, Jami’in Hulda da Jama’a na rundunar, DSP Buhari Abdullahi, ya ce harin ya faru ne a kauyukan Rahama, Lambo da Garin Galadima.

  • An Nada Liu Xianfa Wakilin Musamman Na Gwamnatin Sin Kan Harkokin Afirka
  • Yadda Buƙatun Kwankwaso Suka Tarwatsa Yiwuwar Haɗin Gwuiwa Da APC

Sanarwar ta bayyana cewa harin ya fara ne da safiyar ranar 24 ga Janairu, 2026.

ADVERTISEMENT

“Ranar 24/01/2026 da misalin karfe 02:00 na dare, bayanan da aka samu sun nuna cewa wasu da ake zargin ‘yan bindiga sun kai hari kauyen Rahama ta hanyar Gagarabami, inda suka harbe tare da kashe Tela Bello Ahmadu, mai shekaru 70,” in ji ‘yansanda.

Sanarwar ta kara da cewa maharan daga bisani sun sace ‘ya’yansa biyu, Saleh Tela (mai shekaru 25) da Abdullahi Tela (mai shekaru 35).

LABARAI MASU NASABA

IGP Disu Ya Hana Jami’an Ƴansanda Yin Amfani Da TikTok Da Instagram Da Sauransu

Gwanjon Kadarori: Kotun Daukaka Kara Ta Kori Karar Da Sani Sha’aban Ya Shigar

Abdullahi ya ce wannan kungiya ta tafi kauyen Lambo da misalin karfe 3:40 na dare, inda suka sace wasu mazauna uku.

“Sun sace Babayo Garba, mai shekaru 30, Malam Abba Musa, mai shekaru 45, da Baayo Bayi, mai shekaru 20,” in ji shi.

Bayan karbar kiran agaji, kungiyoyin sintirin ‘yansanda karkashin Operation Hattara, tare da hadin gwiwar mafarauta da ‘yan sa-kai, sun tafi wurin suka yi arangama da maharan.

“Yayin aikin, Baayo Bayi, abin takaici, ya fada cikin musayar wuta kuma daga baya aka tabbatar da rasuwarsa, yayin da Babayo Garba da Malam Abba Musaaka ceto su lafiya,” in ji sanarwar.

‘Yansanda sun ce an kashe wasu daga cikin maharan uku yayin musayar wuta, yayin da sauran suka tsere zuwa cikin daji, inda ake zargin sun samu raunuka daga harbin bindiga.

Abubuwan da aka kwato daga aikin sun hada da: bindigogi AK-47 guda biyu, jigida guda hudu, harsasai 68 na 7.62mm, harsasai 120 da aka harba, babura guda hudu da kuma kudi Naira 2,300.

An kai wadanda aka ceto asibiti domin gwajin lafiya.

Rundunar ta ce an kara kokari wajen kama maharan da suka tsere, sannan za a sanar da al’umma da zarar an samu ci gaba.

Kwamishinan ‘Yansanda, CP Umar Ahmed Chuso, ya tabbatar wa mazauna jihar cewa rundunar na nan daram wajen tabbatar da tsaro.

“Ya tabbatar wa jama’a cewa rundunar ba za ta yi kasa a gwiwa wajen kare rayuka da dukiyoyi a fadin jihar ba, sannan ya yi kira ga jama’a da su ci gaba da ba da goyon baya ta hanyar samar da sahihan bayanai cikin lokaci ga ‘yansanda,” in ji sanarwar.

Gombe
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Wasu Fusatattun Mutane Sun Lakaɗa Wa Mutum Biyu Duka Har Lahira A Kaduna
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Mun Ɗauki Nauyin Karatun Masu Digiri Ta Hanyar Sayar Da Ƙosai Da Ƙuli-ƙuli —Wasu Ƴan Kasuwa
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Adadin Mutanen Da Tsananin Zafi Ya Kashe A Turai Ya Haura Dubu 1,300 —WHO
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan

MASU ALAKA

Disu
Kotu Da Ɗansanda

IGP Disu Ya Hana Jami’an Ƴansanda Yin Amfani Da TikTok Da Instagram Da Sauransu

June 26, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga
Kotu Da Ɗansanda

Gwanjon Kadarori: Kotun Daukaka Kara Ta Kori Karar Da Sani Sha’aban Ya Shigar

June 18, 2026
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa
Kotu Da Ɗansanda

’Yansanda Sun Ceto Yaro Mai Shekara Shida Da Aka Sace, Sun Cafke Wanda Ake Zargi A Borno

June 13, 2026
Next Post
Za A Fuskanci Karancin Motoci A Nijeriya Sakamakon Karin Haraji

Wani Direba Da Ya Buge Mai PoS Har Lahira Ya Tsere A Abuja

LABARAI MASU NASABA

ADC Ta Nemi A Binciki Nafiu Bala Bayan INEC Ta Ƙaryata Iƙirarinsa

ADC Ta Nemi A Binciki Nafiu Bala Bayan INEC Ta Ƙaryata Iƙirarinsa

July 14, 2026
Sojoji Sun Kashe ’Yan Ta’adda 3, Sun Ƙwato Makamai A Sakkwato

Sojoji Sun Daƙile Harin ISWAP A Borno

July 14, 2026
Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya

Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya

July 14, 2026
Tsaka mai wuyar Infantino da Koma bayan mulkin yamma

Tsaka mai wuyar Infantino da Koma bayan mulkin yamma

July 14, 2026
“Buhari Ya Taɓa tambaya Ta Mutane Nawa Na Kashe Saboda Yawan Azumin Dana Ke Yi”

“Buhari Ya Taɓa tambaya Ta Mutane Nawa Na Kashe Saboda Yawan Azumin Dana Ke Yi”

July 14, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Ce Za A Gurfanar Da Tubabbun ’Yan ta’addan Da Suka Sake Aikata Manyan Laifuka

Gwamnatin Tarayya Ta Ce Za A Gurfanar Da Tubabbun ’Yan ta’addan Da Suka Sake Aikata Manyan Laifuka

July 14, 2026
Tinubu Ya Gana da Gwamnan Kwara Bayan Harin Ta’addanci Da Ya Yi Ajalin Sama Da Mutane 160

Kyawawan Manufofin Buhari Za Su Ci Gaba Da Yi Wa ’Yan Nijeriya Tasiri – Tinubu

July 14, 2026
Abin Da Ake Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin” Da Aka Yanke Wa Sin Na Kashin Kanta Ba Shi Da Wani Amfani

Abin Da Ake Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin” Da Aka Yanke Wa Sin Na Kashin Kanta Ba Shi Da Wani Amfani

July 13, 2026
Tafiye-tafiyen Fasinjojin Jirgin Kasa A Kasar Sin Sun Haura Biliyan 2.3 A Rabin Farko Na Bana

Tafiye-tafiyen Fasinjojin Jirgin Kasa A Kasar Sin Sun Haura Biliyan 2.3 A Rabin Farko Na Bana

July 13, 2026
Gwamnatin Tarayya Za Ta Ƙaddamar Da Tsarin Daƙile Rugujewar Gine-Gine

Gwamnatin Tarayya Za Ta Ƙaddamar Da Tsarin Daƙile Rugujewar Gine-Gine

July 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.