ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Bindiga: ‘Yansanda Sun Ceto Mutum Uku Gami Da Kwato Bindigar AK-47 A Gombe

by Rabi'u Ali Indabawa
5 months ago
Gombe

Rundunar ‘Yansandan Jihar Gombe ta ceto mutum uku da aka sace tare da kwato bindigogi AK-47 guda biyu, bayan wani hari da ake zargin ‘yan bindiga ne suka kai a Gundumar Pindiga da ke Karamar Hukumar Akko a jihar.

A cikin wata sanarwa da rundunar ta fitar, Jami’in Hulda da Jama’a na rundunar, DSP Buhari Abdullahi, ya ce harin ya faru ne a kauyukan Rahama, Lambo da Garin Galadima.

  • An Nada Liu Xianfa Wakilin Musamman Na Gwamnatin Sin Kan Harkokin Afirka
  • Yadda Buƙatun Kwankwaso Suka Tarwatsa Yiwuwar Haɗin Gwuiwa Da APC

Sanarwar ta bayyana cewa harin ya fara ne da safiyar ranar 24 ga Janairu, 2026.

ADVERTISEMENT

“Ranar 24/01/2026 da misalin karfe 02:00 na dare, bayanan da aka samu sun nuna cewa wasu da ake zargin ‘yan bindiga sun kai hari kauyen Rahama ta hanyar Gagarabami, inda suka harbe tare da kashe Tela Bello Ahmadu, mai shekaru 70,” in ji ‘yansanda.

Sanarwar ta kara da cewa maharan daga bisani sun sace ‘ya’yansa biyu, Saleh Tela (mai shekaru 25) da Abdullahi Tela (mai shekaru 35).

LABARAI MASU NASABA

Gwanjon Kadarori: Kotun Daukaka Kara Ta Kori Karar Da Sani Sha’aban Ya Shigar

’Yansanda Sun Ceto Yaro Mai Shekara Shida Da Aka Sace, Sun Cafke Wanda Ake Zargi A Borno

Abdullahi ya ce wannan kungiya ta tafi kauyen Lambo da misalin karfe 3:40 na dare, inda suka sace wasu mazauna uku.

“Sun sace Babayo Garba, mai shekaru 30, Malam Abba Musa, mai shekaru 45, da Baayo Bayi, mai shekaru 20,” in ji shi.

Bayan karbar kiran agaji, kungiyoyin sintirin ‘yansanda karkashin Operation Hattara, tare da hadin gwiwar mafarauta da ‘yan sa-kai, sun tafi wurin suka yi arangama da maharan.

“Yayin aikin, Baayo Bayi, abin takaici, ya fada cikin musayar wuta kuma daga baya aka tabbatar da rasuwarsa, yayin da Babayo Garba da Malam Abba Musaaka ceto su lafiya,” in ji sanarwar.

‘Yansanda sun ce an kashe wasu daga cikin maharan uku yayin musayar wuta, yayin da sauran suka tsere zuwa cikin daji, inda ake zargin sun samu raunuka daga harbin bindiga.

Abubuwan da aka kwato daga aikin sun hada da: bindigogi AK-47 guda biyu, jigida guda hudu, harsasai 68 na 7.62mm, harsasai 120 da aka harba, babura guda hudu da kuma kudi Naira 2,300.

An kai wadanda aka ceto asibiti domin gwajin lafiya.

Rundunar ta ce an kara kokari wajen kama maharan da suka tsere, sannan za a sanar da al’umma da zarar an samu ci gaba.

Kwamishinan ‘Yansanda, CP Umar Ahmed Chuso, ya tabbatar wa mazauna jihar cewa rundunar na nan daram wajen tabbatar da tsaro.

“Ya tabbatar wa jama’a cewa rundunar ba za ta yi kasa a gwiwa wajen kare rayuka da dukiyoyi a fadin jihar ba, sannan ya yi kira ga jama’a da su ci gaba da ba da goyon baya ta hanyar samar da sahihan bayanai cikin lokaci ga ‘yansanda,” in ji sanarwar.

Gombe
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Nijar Ta Rattaba Hannu A Kan Dokar Haramta Auren Jinsi
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Za Mu Iya Sayar Da Manmu Ba Tare Da Wata Matsala Ba -Iran
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Dattawan Arewa Sun Buƙaci Tinubu Ya Ayyana Dokar Ta-baci Kan Tabarbarewar Tsaro
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Nijeriya Ta Karbi Ƴan Nijeriya 268 Da Suka Tsero Daga Afirka Ta Kudu

MASU ALAKA

Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga
Kotu Da Ɗansanda

Gwanjon Kadarori: Kotun Daukaka Kara Ta Kori Karar Da Sani Sha’aban Ya Shigar

June 18, 2026
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa
Kotu Da Ɗansanda

’Yansanda Sun Ceto Yaro Mai Shekara Shida Da Aka Sace, Sun Cafke Wanda Ake Zargi A Borno

June 13, 2026
An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya
Kotu Da Ɗansanda

An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

June 13, 2026
Next Post
Za A Fuskanci Karancin Motoci A Nijeriya Sakamakon Karin Haraji

Wani Direba Da Ya Buge Mai PoS Har Lahira Ya Tsere A Abuja

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026
Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

June 23, 2026
Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

June 23, 2026
Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

June 23, 2026
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

’Yansanda Sun Kama Mutane 57 Da Ake Zargi Da Ayyukan Ta’addanci A Adamawa

June 23, 2026
Li Qiang Ya Gana Da Firaministan Kasar Guinea

Li Qiang Ya Gana Da Firaministan Kasar Guinea

June 23, 2026
Maniyyatan Nijeriya

Hajjin 2026: NAHCON Ta Kammala Jigilar Alhazan Nijeriya Daga Saudiyya

June 23, 2026
Kamfanin Sin Ya Kammala Babban Aikin Samar Da Ruwa A Babban Birnin Nijeriya

Kamfanin Sin Ya Kammala Babban Aikin Samar Da Ruwa A Babban Birnin Nijeriya

June 23, 2026
Binciken CGTN: Fasahohin Zamani Sun Habaka Ayyuka Yayin Da Tsarin Cin Moriya Tare Ya Yi Fintinkau

Binciken CGTN: Fasahohin Zamani Sun Habaka Ayyuka Yayin Da Tsarin Cin Moriya Tare Ya Yi Fintinkau

June 23, 2026
'Yan Bindiga

Yan Bindiga Sun Kashe Manoma Shida A Birnin Gwari Ta Jihar Kaduna

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.