ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Bindiga: ‘Yansanda Sun Ceto Mutum Uku Gami Da Kwato Bindigar AK-47 A Gombe

by Rabi'u Ali Indabawa
4 months ago
Gombe

Rundunar ‘Yansandan Jihar Gombe ta ceto mutum uku da aka sace tare da kwato bindigogi AK-47 guda biyu, bayan wani hari da ake zargin ‘yan bindiga ne suka kai a Gundumar Pindiga da ke Karamar Hukumar Akko a jihar.

A cikin wata sanarwa da rundunar ta fitar, Jami’in Hulda da Jama’a na rundunar, DSP Buhari Abdullahi, ya ce harin ya faru ne a kauyukan Rahama, Lambo da Garin Galadima.

  • An Nada Liu Xianfa Wakilin Musamman Na Gwamnatin Sin Kan Harkokin Afirka
  • Yadda Buƙatun Kwankwaso Suka Tarwatsa Yiwuwar Haɗin Gwuiwa Da APC

Sanarwar ta bayyana cewa harin ya fara ne da safiyar ranar 24 ga Janairu, 2026.

ADVERTISEMENT

“Ranar 24/01/2026 da misalin karfe 02:00 na dare, bayanan da aka samu sun nuna cewa wasu da ake zargin ‘yan bindiga sun kai hari kauyen Rahama ta hanyar Gagarabami, inda suka harbe tare da kashe Tela Bello Ahmadu, mai shekaru 70,” in ji ‘yansanda.

Sanarwar ta kara da cewa maharan daga bisani sun sace ‘ya’yansa biyu, Saleh Tela (mai shekaru 25) da Abdullahi Tela (mai shekaru 35).

LABARAI MASU NASABA

An Kashe Wani Mamba Na NYSC A Harin Fashi Da Makami A Abuja

An Cafke Mutum 7 Kan Satar Waya Da Fasa Gidaje A Jihar Yobe

Abdullahi ya ce wannan kungiya ta tafi kauyen Lambo da misalin karfe 3:40 na dare, inda suka sace wasu mazauna uku.

“Sun sace Babayo Garba, mai shekaru 30, Malam Abba Musa, mai shekaru 45, da Baayo Bayi, mai shekaru 20,” in ji shi.

Bayan karbar kiran agaji, kungiyoyin sintirin ‘yansanda karkashin Operation Hattara, tare da hadin gwiwar mafarauta da ‘yan sa-kai, sun tafi wurin suka yi arangama da maharan.

“Yayin aikin, Baayo Bayi, abin takaici, ya fada cikin musayar wuta kuma daga baya aka tabbatar da rasuwarsa, yayin da Babayo Garba da Malam Abba Musaaka ceto su lafiya,” in ji sanarwar.

‘Yansanda sun ce an kashe wasu daga cikin maharan uku yayin musayar wuta, yayin da sauran suka tsere zuwa cikin daji, inda ake zargin sun samu raunuka daga harbin bindiga.

Abubuwan da aka kwato daga aikin sun hada da: bindigogi AK-47 guda biyu, jigida guda hudu, harsasai 68 na 7.62mm, harsasai 120 da aka harba, babura guda hudu da kuma kudi Naira 2,300.

An kai wadanda aka ceto asibiti domin gwajin lafiya.

Rundunar ta ce an kara kokari wajen kama maharan da suka tsere, sannan za a sanar da al’umma da zarar an samu ci gaba.

Kwamishinan ‘Yansanda, CP Umar Ahmed Chuso, ya tabbatar wa mazauna jihar cewa rundunar na nan daram wajen tabbatar da tsaro.

“Ya tabbatar wa jama’a cewa rundunar ba za ta yi kasa a gwiwa wajen kare rayuka da dukiyoyi a fadin jihar ba, sannan ya yi kira ga jama’a da su ci gaba da ba da goyon baya ta hanyar samar da sahihan bayanai cikin lokaci ga ‘yansanda,” in ji sanarwar.

Gombe
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    NSCDC Ta Cafke Mutum 10 Da Ake Zargi Da Satar Kayan Gwamnati Da Kuma Fashi A Kano
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƴansanda Su Ƙi Karɓar Cin Hancin Naira Miliyan 500 Daga Hannun Dillalin Miyagun Ƙwayoyi
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƙasashen DR Congo Uganda Da Sudan Sun Haɗa Kai Domin Yaƙar Ibola
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Zafin Rana Ya Yi Ajalin Mutum 16 A Indiya

MASU ALAKA

An Kashe Wani Mamba Na NYSC A Harin Fashi Da Makami A Abuja
Kotu Da Ɗansanda

An Kashe Wani Mamba Na NYSC A Harin Fashi Da Makami A Abuja

May 2, 2026
An Kama Matashi A Kano Kan Zargin Kashe Abokinsa
Kotu Da Ɗansanda

An Cafke Mutum 7 Kan Satar Waya Da Fasa Gidaje A Jihar Yobe

April 25, 2026
An Sake Samun Gawar Wani Dan Nijeriya A Gidansa Da Ke Burtaniya
Kotu Da Ɗansanda

An Sake Samun Gawar Wani Dan Nijeriya A Gidansa Da Ke Burtaniya

April 25, 2026
Next Post
Za A Fuskanci Karancin Motoci A Nijeriya Sakamakon Karin Haraji

Wani Direba Da Ya Buge Mai PoS Har Lahira Ya Tsere A Abuja

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026
An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.