Ƙungiyar ƴan majalisar wakilai na jam’iyyar ADC ta buƙaci a gurfanar da shugaban hukumar zaɓe mai zaman kanta ta ƙasa (INEC), Farfesa Joash Amupitan, kan zargin nuna son kai da rashin daidaito a matsayin mai kula da zaɓe.
Shugaban ƙungiyar ADC, Hon. Ɓictor Ogene, ya bayyana wannan a Abuja yayin da yake ba da bayanai kan sakamakon taron farko na ƙungiyar da aka gudanar a ranar Lahadi, 12 ga Afrilu, 2026, don duba harkokin siyasa a ƙasa nan.
ADC Ta Nemi Shugaban INEC Ya Yi Murabus
Kabiru Marafa Ya Jagoranci Daruruwan Mabiyansa Zuwa ADC A Zamfara
A taron, ƙungiyar ta nuna damuwa game da son kai da ɓangaranci na shugaban hukumar zaɓe, Farfesa Joash Amupitan, wajen sa ido kan zaɓukan 2027. Wannan ya biye bayan wasu bayanai da ayyuka na baya-bayan nan daga shugaban da ake ganin yana kawo tarnaƙi da nuna son kai, da kauce wa ƙa’idojin aikin hukumar.
“An zargi cewa a baya ya yi wata magana ta jam’iyya a shafina na Tuwita, inda ya nuna goyon baya ga jam’iyyar APC wadda ke mulki.
“Bugu da ƙari, an zargi shi da saka abubuwan da ke tuhumar kisan ƙare dangi kan Kiristoci a Nijeriya. Ko da yake INEC ta musanta cewa Farfesa Amupitan ne mai asusun da ake magana a kai, sai dai binciken da aka yi kan lamarin ta wurin majiyoyi daban-daban sun nuna cewa Shafin nasa ne, kuma lambar wayar da aka yi amfani da ita wajen ƙirƙirar shafin sunansa ne.
“Wannan ya jawo damuwa game da gaskiyarsa, riƙon amana, da amintaccensa, musamman la’akari da muhimmancin muƙamin da yake riƙe da shi, wanda zai yi tasiri mai zurfi ga ƙasa,” in ji ƙungiyar.















Discussion about this post