ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 6, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ɗaliban Northwest Kano Sun Yi Zanga-Zanga Kan Ƙarin Kuɗin Makaranta

by Abubakar Sulaiman
1 year ago
Kano

Ɗaliban Jami’ar Northwest da ke Kano sun gudanar da zanga-zanga biyo bayan ƙarin kuɗin makaranta da ya kai kusan kashi 200%, inda aka ɗaga kuɗin dadaga ₦19,700 zuwa ₦57,300 a sabuwar shekarar karatu ta 2024/2025. Wannan ƙarin ya haifar da fargaba a tsakanin ɗalibai da iyayensu musamman a yanayin matsin tattalin arziƙin da Nijeriya ke ciki.

Ƙungiyar Ɗalibai ta Jami’ar (SUG), a cikin wata sanarwa da shugaban ta, Abdussalam Mahmoud Ahmad, ya sanya wa hannu, ta bayyana cewa ta fahimci nauyin da ƙarin kuɗin ya ɗora wa ɗalibai. Ya ce “muna bibiyar duk wata hanya da za ta taimaka wajen neman mafita mai sauƙin da rage raɗaɗi,” duk da cewa ba su bayar da takamaiman lokacin da za a warware lamarin ba.

  • Sanatocin Arewa Sun Yi Jimamin Rasuwar ‘Yan Wasan Kano
  • Ma’aikatar Tsaron Kasar Sin Ta Maida Martani Game Da Munanan Kalaman Sakataren Tsaron Amurka Kan Kasar Sin

Wannan ƙarin kuɗin ya ƙara tayar da ƙura a tsakanin ɗalibai da iyayensu duba da yadda farashin karatu ke ci gaba da tashi a jami’o’i a faɗin ƙasar. Ɗalibai da dama sun bayyana fushinsu a kafafen sada zumunta, musamman a X (Twitter), inda aka fara amfani da taken #NWUFeeProtest.

ADVERTISEMENT

Izuwa yanzu, ba a ji wani bayani daga mahukuntan jami’ar ba dangane da dalilin wannan gagarumin ƙarin kuɗin lokac guda. Ƙungiyar Ɗalibai ta buƙaci a kwantar da hankali, tare da buƙatar dalibai su gabatar da ƙorafinsu kai tsaye zuwa ofisoshin ƙungiyar dake harabar Muhammadu Buhari Way Main Campus ko Ado Bayero House City Campus.

Wannan rikici ya ƙara bayyana yadda matsin tattalin arziƙi da rashin fayyace manufofi ke ci gaba da kawo cikas ga tsarin ilimi a Nijeriya, inda ɗalibai ke fama da ƙarin kuɗin makaranta da kuma ƙarancin tallafi daga hukumomi.

LABARAI MASU NASABA

Mulkin Tinubu A Shekara 3:Ina Aka Fito? Ina Aka Dosa?

Har Yanzu Akwai Sauran Rina A Kaba Game Da Makomar Yara A Nijeriya

Kano
Abubakar Sulaiman
Website |  + postsBio
  • Abubakar Sulaiman
    Sace Ɗalibai Ya Karu A Mulkin Tinubu Fiye Da Gwamnatocin Baya – Obi
  • Abubakar Sulaiman
    Ƴansanda Sun Daƙile Yunƙurin Garkuwa Da Wasu Ma’aurata A Abuja
  • Abubakar Sulaiman
    Sabon Rikicin Manoma Da Makiyaya yayi Ajalin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi
  • Abubakar Sulaiman
    Hajji 2026: Mahajjata 1,905 Sun Dawo Nijeriya Daga Saudiyya

MASU ALAKA

Babu Wani Shiri Na Kwaso ‘Yan Nijeriya Daga Falasdin Ko Isra’ila –Gwamnatin Tarayya
Manyan Labarai

Mulkin Tinubu A Shekara 3:Ina Aka Fito? Ina Aka Dosa?

June 5, 2026
Har Yanzu Akwai Sauran Rina A Kaba Game Da Makomar Yara A Nijeriya
Manyan Labarai

Har Yanzu Akwai Sauran Rina A Kaba Game Da Makomar Yara A Nijeriya

June 5, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi
Manyan Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Next Post
Jirgin Sojoji Yayi Kuskuren Buɗe Wuta Kan Ƴan Sa Kai A Maru

Jirgin Sojoji Yayi Kuskuren Buɗe Wuta Kan Ƴan Sa Kai A Maru

LABARAI MASU NASABA

NSCDC Ta Sallami Ma’aikatan Sa-kai Biyar A Kano Saboda Rashin Da’a

NSCDC Ta Sallami Ma’aikatan Sa-kai Biyar A Kano Saboda Rashin Da’a

June 6, 2026
Manoma 67 Suka Amfana Da Horon Cibiyar  NIHORT

Manoma 67 Suka Amfana Da Horon Cibiyar  NIHORT

June 6, 2026
Sace Ɗalibai Ya Karu A Mulkin Tinubu Fiye Da Gwamnatocin Baya – Obi

Sace Ɗalibai Ya Karu A Mulkin Tinubu Fiye Da Gwamnatocin Baya – Obi

June 6, 2026
Dalilan Da Suka Sa Fannin Kiwo Ke Fuskantar Kalubale A Nijeriya —Gwamnatin Tarayya

Dalilan Da Suka Sa Fannin Kiwo Ke Fuskantar Kalubale A Nijeriya —Gwamnatin Tarayya

June 6, 2026
Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Na Harkokin Kasuwanci

Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Na Harkokin Kasuwanci

June 5, 2026
Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP

Zaben Fitar Da Gwani Na APC: Tinubu Zai Shiga Tsakani Wajen Warware Rikicin Jam’iyyar

June 5, 2026
Ma’aikatar Wajen Sin Ta Yi Karin Bayani Game Da Ziyarar Da Xi Zai Yi A Koriya Ta Arewa

Ma’aikatar Wajen Sin Ta Yi Karin Bayani Game Da Ziyarar Da Xi Zai Yi A Koriya Ta Arewa

June 5, 2026
2027:Gwamnoni Na Fuskantar Turjiya Wajen Gwagwarmayar Kare Kujerunsu Da Kuma Samar Da Magadansu

2027:Gwamnoni Na Fuskantar Turjiya Wajen Gwagwarmayar Kare Kujerunsu Da Kuma Samar Da Magadansu

June 5, 2026
An Fitar Da “Rahoton Yanayin Muhalli Na Kasar Sin Na 2025”

An Fitar Da “Rahoton Yanayin Muhalli Na Kasar Sin Na 2025”

June 5, 2026
Abubuwan Da Ba A Fada Ba Game Da Sace Janar Rabe Abubakar A Katsi

Abubuwan Da Ba A Fada Ba Game Da Sace Janar Rabe Abubakar A Katsi

June 5, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.