ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Batun Kudurin ‘Yan Majalisar Amurka Kan Kwankwaso Da Fulani Makiyaya

by Leadership Hausa and Sulaiman
5 months ago
The U.S. Congress is seen on Tuesday, April 23, 2019, Washington, D.C.  (Photo by Aurora Samperio/NurPhoto via Getty Images)

The U.S. Congress is seen on Tuesday, April 23, 2019, Washington, D.C. (Photo by Aurora Samperio/NurPhoto via Getty Images)

‘Yan Majalisar kasar Amurka na jam’iyyar Republican, a ranar 11 ga watan Fabirairun  2026, sun gabatar da wani kuduri kan bukatar, a kakabawa tsohon gwaman jihar Kano Dakta Rabiu Kwankwaso da kuma wani sashe, na ‘yan kabliyar Fulani, da ‘yan majalisar, suka yi ikiran cewa, ‘yan ta’adda ne, takunkumi.

Sun gabatar da wannan kudurin na su ne dai, bisa kafa hujjarsu kan zargin sarkakiyar yin amfani da addini wajen yin hukunci da kuma tauye hakkin bill adama, musamman a Arewacin kasar nan.

  • Makomar Nijeriya Na Hannun FIFA – Shehu Dikko
  • Jerin Sharuddan Da Chelle Ya Gindayawa NFF Domin Cigaba Da Jagorantar Super Eagles 

Kudurin na su, ya kuma bukaci da a  wanzar da dokar bayar da damar ‘yancin gudanar da addini, ba tare da wata tsangwama ba, inda kuma, suka bukaci da a kakabawa kadarorin Kwakwaso da kuma soke katin bizarsa.

ADVERTISEMENT

Duba da cewa, wannan kudurin na ‘yan majalisar, ya kasance tamkar wani yinkuri ne, na tauye ‘yancin marasa karfi, hakan ya Dabo ya  kuma haifar da mummunar ce-ce kuce, a Bangaren huddar difolomasiyya ta kasa da kasa, tare da kuma bijero da tambayoyi, kan yin katsalandan daga ketare, kan lamarin da ya shafi kasar nan.

Wannan Jaridar ta yi nazari kan illolin da ke tattare da wannan kudurin na’yan majalisar, musamman ganin cewa, kudurin, ya karkata ne, kan wani Bangaren daya kawai wanda hakan ya kuma nuna cewa, ana bukatar sauye-sauye ne kawai na cikin gida, ba wai hasashen ‘yan bani na iya, daga ketare ba.

LABARAI MASU NASABA

Ana Ci Gaba Da Tafka Muhawara Kan Shirin Gwamnati Na Haramta Masana’atun Sarrafa Robobi

Kisan Gillar Marabar Jos: Bai Kamata Jinin Malama Ummulkhairi Ya Tafi A Banza Ba

Kazalika, wannan kudurin, bai da wata nasaba da karancin ci gaba da tashen da Kwankwaso ke ci gaba da samu, a fagen siyasar jiharsa ta Kano ba ne ko kuma yawan sukar wasu tsare-tsaren gwamnatin tarayya ba ne, da kuma yadda a karkashin tafiyarsa a karkashin ta Kwankwasiyya, da ke ci gaba da kare muradun Arewacin kasar nan ba.

Masu yin sukar adawa a majalisar ta Amurka suna kawai danganta Kwankwaso, da wanzarwa da kuma ganin, an kaddamar da Shari’a Musulunci, a birnin na Dabo, inda ake yanke hukunci, kan duk wanda ya yi wani Batanci, kan Manzo Allah SAW, inda kuma aukuwar rikice-rikice, ka janyo hankalin kasashen duniya.

Bugu da kari, sanya jagororin ‘yan kabilar Fulani a cikin jeren ‘yan ta’adda, hakan ya nuna zargin da ake yiwa Fulani Makiyaya, a matsayin wadanda, ke janyo rikice-rikicen manoma da Fulani Makiyaya a kasar, amma abin takaicin, sai aka danganta hakan a matsayin, aukuwar rikice-rikicen addini.

Sai dai, za a iya  irin wadannan rikice-rikicen, sun samo asali ne daga karancin kudade da sauyin yanayi da kuma gazawar, iya gudanar da shuganci na gari a kasar.

Dangane da wasu alkaluma da aka samu daga yankunan da ake sanun aukuwar rikice-rikicen da ake yin amfani da makamai wato ACLED, sun nuna cewa, akwai hannun wasu Fulani Makiyaya, musamman kan batun kokarin samu wajen yin kiwon dabbobi fiye da batun rikicin addini.

Nijeriya dai, ta sha kin amince wa da duk wani yunkuri, na yi mata katsalandan, a cikin al’amuranta, daga ketare, musamman wanda hakan, ke kunshe, a cikin kundin tsarin mulkin kasar na 1999 da aka sabunta da kuma yarjejeniyar kare ‘yancin bil’Adama ta Afirka

Kakaba takunkimi ga wasu fitatfitattun ‘yan siyasa musammna rinsu Kwankwaso za a iya cewa, wata bita da kullin siyasa, musamman duba da cewa, zaBen shugaban kasa, na 2027 na kara kunno ka.

Hakazalika, akwai kuma batun kara karfafa huddar Jakadanci, a tsakanin Nijeriya da kasar Amurka, wadda take kara neman hadin kan Nijeriya, kan dakile ta’addanci na kasa da kasa da kuma daidaita al’amura a yankin Sahel.

A Bangaren tattalin arziki kuwa, za a iya cewa, wannan kudurin na ‘yan majalisar Amurka ta kakabawa kadarorin Kwakwaso takukumi da kuma soke katin bizarsa, a namu ra’ayin hakan zai kawo cikas ga zuba jari a jihohin da ke Arewacin kasar, musamman ganin cewa, daukakar da Kwankaso yake da ita a yankin, na nan daram-dam

Birnin na Dabo dai, na ci gba da amsa sunansa, na yankin da ya yi karfi, a fagane hada-hadar kasuwanci, ba wai kawai a Kanon kadai ba, har da ketare, wanda hakan ke nuna cewa duk wani yunkuri na kawo koma bayan ci gaba da gudanar da hada-hadar kasuwanci a jihar, hakan zai kara haifar da mummunar matsin tattalin arziki, musamman duba da yadda tuni, kalubalen rashin tsaro, ya yi kamari.

A zahirance dai, wannan kudurin, ya karkata ne, kan Sharia’r Musulunci da kuma kan Fulani Makiyaya, inda hakan ke ci  gaba dora alamar tambaya, na rashin yin adalci.

Kasar nan dai, na gudanar da tsari biyu na Bangaren Shari’a wanda ake wanzar da Shari’ar kan lamaru na kasshin kai da kuma a Bangaren batutuwan da suka shafi, aikata manyan laifuka, tun a lokacin da ake da jihohi 12 a Arewacin kasar, wato tun a 2000.

Wannan tsarin dai, an samar da shi ne, tun lokacin da aka rarraba kasar a 1914 wanda ya bai wa Musulmai, damar gudanar da lamauransu, a bisa tsarin tarayya.

Kazalika, tun a lokacin da turawan mulikin mallaka, suka jagoranci kasar, musamman a lokacin Lord Lugard, mulkinsa ya bai wa Musulmai, damar tafiyar da lamauransu, kan turbar Shari’a, inda aka samar da kotunan Muslunci da ke yankewa Musulmai zalla, hukunci.

Batun na daukar doka a hannun da Musulmai ke yi, ga duk wanda ya yi Batanci kan Manzo Allah SAW, za iya cewa, hakan na faruwa ne, saboda sakacin gwamnati, na daukar matakin gaggawa ga duk wanda ya aikata wannan laifin.

Wani abinda dubi a nan shi ne, su kansu Fulani Makiyaya, ba su tsira wajen zamowa wacanda ‘yan bindiga, ke kai wa hare-hare ba, tare da kuma yadda matsalar sauyin yanayi, ke shafar rayuwarsu, har ta kai ga, ta tilasa ta su, barin matsugunan su.

Alumma da dama da Arewacin Nijeriya, kalubalen rashin tsaro, ya raba su, da rayuwarsu cikinsu har da kuma wasu mabiya addinin Kirista.

An kuma samu rahotanni da ban da ban na kai hare-hare, a guraren da ake gudanar da ibada, a saboda haka, ya zama wajibi, Nijeriya ta shi tsaye, ta tunkaro magance kalubalen rashin tsaron, da ya jima, yana addabar kasar.

Bugu da kari, dole ne gwamnatin kasar nan, ta tsaya kai da fata wajen kin amincewa, da wannan kudurin na ‘yan majalisar Amurka.

Suma gwamnonin da ke a Arewa, dole ne, su samar da wani tsarin tabbatar da tsaro, a cikin yankunan su, kmaar da irin sabon tsarin da gwamnatin Kaduna mai ci, ta kirkiro da shi, na  kara wanzar da tsaro, wanda akalla, ya rage samun aukuwar matsalar tsaro, har kusan kaso 25, a shekarun da suka wuce.

Akwai bukatar ta hanyar yin amfani da ofishin mai bai wa shugaban kasa shawara kan lamarin tsaro, a saita lamura, musamman kan lalubo da mafita, kan batun talauci da sauyin yanayi, duba da cewa, wadannan batutuwan biyu, na dga matsalar, da ke kara haddasa aukuwar rikice-rikice, a tsakanin manoma da Fulani Makiyaya.

Kazalika, ya kamata kasar ta kara karfafa huddalar diflomasiyya da Amurka da kuma kungiyar nahiyar Afirka wato AU musamman wajen samar da sauye-sauye, masu dorewa a cikin kasar nan.

Wannan barazanar ta ‘yan majalisar Amurka, da suka auna ta kan Kwankwaso da ‘yan kabilar Fulani, a namu ra’ayin hakan na nuna cewa, ‘yan bani na iya da ke a ketare, son sanya Tabarau dinsu, suna liken kalubalen da Nijeriya ke ciki.

Samun hadin kan kasar dai, ba wai ‘yan tsiraru daga ketare ne, ke da wani ikon, kakabawa wani sashen jinsi na kasar takunkumi ba, amma kamata yayi, mahukuntan kasar, su samar da sauye-sauyen da za su inganta raywar ‘yan kasar

Ta hanyar zuba jari a Bangaren tsaro, musamman a Arewacin Nijeriya da kuma  adaukacin fadin kasar, hakan zai kawar da duk wani tarnaki da kasar ke fuskanta.

Amurka
Leadership Hausa
Website |  + posts Bio
  • Leadership Hausa
    Tallafa Wa Yara Masu Buƙatu Na Musamman Shi Ne Burina
  • Leadership Hausa
    Dole Mata Su Rungumi Sana’o’i Domin Tsira Daga Takaicin Zamani —Ramatu Bello
  • Leadership Hausa
    Batun Dakile Shan Taba Sigari A Tsakanin Yara A Nijeriya
  • Leadership Hausa
    Har Yanzu Akwai Sauran Rina A Kaba Game Da Makomar Yara A Nijeriya
Amurka
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya
  • Sulaiman
    Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026
  • Sulaiman
    An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”
  • Sulaiman
    Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

MASU ALAKA

Ana Ci Gaba Da Tafka Muhawara Kan Shirin Gwamnati Na Haramta Masana’atun Sarrafa Robobi
Ra'ayinmu

Ana Ci Gaba Da Tafka Muhawara Kan Shirin Gwamnati Na Haramta Masana’atun Sarrafa Robobi

July 10, 2026
Kisan Gillar Marabar Jos: Bai Kamata Jinin Malama Ummulkhairi Ya Tafi A Banza Ba
Ra'ayinmu

Kisan Gillar Marabar Jos: Bai Kamata Jinin Malama Ummulkhairi Ya Tafi A Banza Ba

July 3, 2026
sikila
Ra'ayinmu

Buƙatar Mayar Da Hankali Wajen Kawo Ƙarshen Ciwon Sikila A Nijeriya

June 26, 2026
Next Post
Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 33 A Kebbi

Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 33 A Kebbi

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026
Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

July 14, 2026
Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.