ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Matsalar Tsaro: Bukatar Daukar Kwakkwaran Mataki

by Leadership Hausa and Sulaiman
2 years ago
tsaro

Nijeriya ta sake samun kanta a cikin halin tashin hankali, tsoro da alhini, a yayin da rahotanni suke nuna cewa, ‘yan ta’adda dauke da muggan makamai sun yi awon gaba da daruruwan dalibai ‘yan makaranta a wasu jihohin kasar nan, hakan shi ya dawo da hannun agogo baya a kokarin da ake yi na samar da tsaro a kasar nan.

A kwanaki ne ‘yan ta’adda suka sace dalibai 280 da malaman su daga makarantar LEA da ke garin Kuriga, ta Jihar Kaduna.

  • Shugabannin Tsaro Sun Gaza, Ya Kamata Gwamnati Ta Sake Lale – Farfesa Lugga
  • Karin Harajin Amurka Ba Zai Dakile Sashen Kere-Keren Kasar Sin Ba

Hakanan ma wasu da ake zargin ‘yan ta’adda ne sun kai hari yankin Buda da ke karamar hukumar Kajuru duk dai a Jihar Kaduna inda suka yi nasarar sace mutum 61.

ADVERTISEMENT

Duk a ‘yan kwanakin nan, sai gashi kuma ‘yan ta’addar Boko Haram sun yi awon gaba da mata 200 a yankin Gamboru-Ngala da kuma karamar hukumar Dikwa a Jihar Borno.

Rahotanni sun nuna cewa, matan da aka sace na daga cikin ‘yan gudun hijira da ayyukan ta’addanci ya raba su da muhallansu, an kuma sace su ne a yayin da suka shiga daji don neman itacen dafa abinci.
Bugu da kari mun samu rahoton kashe mutum 50 ciki har da iyalai 7 a harin da ‘yan ta’adda suka kai yankin Gbagir da ke karamar hukumar Ukum ta Jihar Benuwai.

LABARAI MASU NASABA

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

A daidai lokacin ne da ‘yan ta’addan ke ci gaba cin karensu babu babbaka sai kuma gashi sun kai hari kauyen Gidan Bakuso da ke karamar hukumar Gada a Jihar Sakkwato, sun kuma yi awon gaba da almajirai ‘yan tsangaya 15 wadanda kuma da dama ba a samu labarinsu ba zuwa yanzu.

A ra’ayin wannan jaridar wadannan ayyuykan ta’addanci ba abin da ya kamata a sa ido ana kallo ba ne; wadannan sun kasance wasu sabbin babi ne a cikin ayyukan ta’addanci da ya addabi sassan Nijeriya a cikin ‘yan shekarun da suka gabata.

Nijeriya ta dade tana dandana kudarta cikin ayyyukan ‘yan ta’adda da ke harkokinsu ba tare da wani tsoro ba a sassan Nijeriya.

Wadannan ayyukan garkuwa da mutane da suka sake kunno kai sun yi matukar tayar da hankulan al’umma, wadanda suka dade suna sauraron alkawuran da aka yi wa ‘yan kasa cewa, lallai za a samar masu da tsaro amma kuma har yanzu babu ranar tabbatar da wancan alkawarin.

A ra’ayinmu, lokaci ya yi da za a canza salon da ake amfani da shi a yaki da ta’addanci a Nijeriya. Duk da cewa, gwamnatin Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ta gaji wasu daga cikin matsalolin tsaron da ake fuskanta, matsalar da take barazana da kokarin jawo masu zuba jari da kuma huldar Nijeriya da kasashen waje.

A ra’ayinmu, duk irin abubuwan da ya shirya gabatarwa na ci gaban kasa, lamarin samar da tsaro shi ya kamata ya zama a sahun gaba don da shi ne tarihi zai kalli yadda ya tafiyar da al’ummar kasa, musamman ma ganin yadda ake kashe mutane ba tare da kakkautawa ba.

Matsayar shugaban kasa ta kin biyan kudin fansa ga ‘yan ta’adda abin a yaba ne, hakan ya yi daidai da yadda ake tafiyar da irin wannan matsalar a sassan duniya yana kuma aikawa da sako mai karfi ga ‘yan ta’addan da ‘yan bindiga cewa, gwamnati a shirye take ta murkushe su.

Amma kuma dole gwamnati ta fito da tsari na musamman na yadda za ta karya alkadarin ‘yan ta’addan ba tare da wani bata lokaci ba.

Tattaunawa da ‘yan ta’adda da kuma ‘yan Bindiga baya haifar da da mai ido, irin tattauanwar tana kara karfafa kungiyoyin ne kawai yana kuma nuna tamkar gwamnati bata da yadda za ta yi ba.
Muna kara jaddada cewa, bai kamata Nijeriya ta nuna gazawa ba a fafatawarta da ‘yan ta’addan da suka gallazawa al’umma ba tare da tausayi ba. Lokacin duk wani tattuanawsa ya wuce, abin da ake bukata a halin yanzu shi ne fafatawa da gungun masu aikata laifi.

Domin samun wannan nasarar, dole ne Shugaba Tinubu ya karfafawa jami’an tsaronmu ta hanyar samar masu da dukkan kayan aiki na zamani daidai da irin wadanda ake amfani da su a kasashen duniya da suka ci gaba. Haka kuma a kwai bukatar a karfafa hanyoyin samar da bayanan sirri don dakile ayyukan ‘yan ta’adda a daidai lokacin da suke shirya ayyukan su.

Har ila yau ya kamata a yi maganin ainihin matsalolin da suke taimakawa wajen bunkasar harkokin ta’addanci a Nijeriya wadanda suka hada da talauci, rashin aikin yi ga matanasu da kuma yadda ake nunawa wasu al’umma wariya a harkokin yau da kullum na kasa.

Ya kamata a samar da ingantaccen tsarin yaki da ta’addanci wanda kuma ya hada da samar da ayyukan bunkasa rayuwar al’umma da suka hada da samar da aikin yi ga matasa, bunkasa bangaren ilimi, kiwon lafiya, da kuma sauraron koke koken al’umma.

Nijeriya kasa ce da ke da al’umma masu aiki tukuru, mun sha fuskantar matsaloli mun kuma yi maganinsu cikin dan kankanin lokaci. Yanzu lokaci ya yi da dukkan dan Nijeriya zai bayar da tasa gundumawar don ganin an kawo karshen ayyukan ‘yan ta’adda da ‘yan bindiga ba tare da nuna bambancin siyasa, kabilanci ko addini ba.

tsaro
Leadership Hausa
Website |  + posts Bio
  • Leadership Hausa
    Yadda Arsenal Ta Lashe Gasar Firimiya Bayan Shekara 22
  • Leadership Hausa
    Bukatar Kawo Karshen Akidar Kyamar Baki A Kasar Afirka Ta Kudu
  • Leadership Hausa
    Ikirarin Cewa Sanata Abdul’aziz Yari Abubakar, Marafan Sokoto, Nauyi Ne Ga Jihar Zamfara Da Jam’iyyar APC Ba Ta Da Tushe
  • Leadership Hausa
    Nazarin Kisan Gillar Da ‘Yan Kato Da Gora Suka Yi Wa Wani Matashi A Biniwe
tsaro
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya
  • Sulaiman
    Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina
  • Sulaiman
    Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026
  • Sulaiman
    Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

MASU ALAKA

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi
Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi
Manyan Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna
Labarai

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Next Post
Mahangar Masana Kan Yawaitar Ibtila’i A Arewa

Mahangar Masana Kan Yawaitar Ibtila'i A Arewa

LABARAI MASU NASABA

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.