• English
  • Business News
Thursday, May 22, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wace Kungiya Ce Za Ta Lashe Kofin Zakarun Turai?

by Abba Ibrahim Wada and Sulaiman
4 weeks ago
in Wasanni
0
UEFA
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kawo yanzu dai kugiyoyin Arsenal da Inter Milan da Barcelona da kuma Paris St-Germain ne suka samu gurbi a wasan kusa da na karshe a Gasar Zakarun Turai wanda hakan ya sa yanzu tunani ya fara komawa kan kungiyar da za ta kafa tarihin lashe gasar, wadda ake sauya wa fasali kuma a ranar 24 ga watan Mayu ne za a buga wasan karshe a birnin Munich na kasar Jamus.

 

A cikin kungiyoyi hudu da suka rage a gasar a yanzu, kungiyoyin Arsenal da PSG sannan tuni masana harkokin wasanni suka fara tsokaci kan kungiyar da suke ganin za ta iya lashe gasar ta bana kasancewar a cikin kungiyoyin da suka rage a gasar Arsenal da Paris Saint German ba su taba lashe gasar ba amma kuma Inter Milan da kungiyar kwallon kafa ta Barcelona duka suna tarihin lashe gasar a baya.

 

Paris St-Germain

Labarai Masu Nasaba

Kocin Super Eagle Ya Gayyaci Ahmed Musa Buga Gasar Kofin Unity A Landan

Tottenham Ta Doke Manchester United A Wasan Karshe Na Europa 

Kungiyar kwallon kafa ta PSG – wadda tuni ta lashe gasar League 1 ta Faransa na daya daga cikin kungiyoyin da ake ganin za su lashe gasar Zakarun Turai ta bana saboda karfin da tawagar take da shi sannan kuma kungiyar a gine take hadi da kwararren mai koyarwa, Luis Enrikue, tsohon kociyan Barcelona da Roma da tawagar kasar Spaniya, yana daya daga cikin kwararrun masu horarwa. Kungiyar za ta kara da Arsenal a wasan na kusa da karshe.

 

Wani shahararren masanin wasanni dan kasar Sifaniya, Guillem Balague na ganin PSG ce za ta lashe gasar. ”Suna da duk wani abu da ake bukata domin lashe kofin, sun iya rike kwallo, a yanzu kungiyar na da karfi, tana da masu kai hari, da na tsakiya haka ma masu tsaron baya”

 

Ya kara da cewa hanya guda da za a iya doke kungiyar ita ce idan ‘yan wasanta suka tare a baya domin tsare gida. ”In dai suka tsananta tsare gida to sai an cinye su, amma idan za su fito, to komai zai iya faruwa” a cewarsa.

 

Sai shi ma Phil McNulty, babban marubucin wasanni na BBC na ganin PSG ce za ta yi nasara a gasar. ”Suna da zaratan ‘‘yan wasa masu kai hari, misali Ousmane Dembele da Khbicha Kbaratskhelia da a yanzu ke kan ganiyarsu, ga kuma Desire Doue da Bradley Barcola wadanda matasan ‘yankwallo ne masu hazaka ”, in ji shi.

 

Inter Milan

Kungiyar kwallon kafa ta Inter Milan, kungiya ce wadda za a iya cewa babu mai kwarinta a kasar Italia domin yanayin yadda take buga wasa da yadda ba ta bari ana zura mata kwallaye a raga abu ne wanda ya kamata a kalla, sannan kuma akwai zakakuran ‘yan wasa da dama da za su taimaka wajen ganin kungiyar ta kai wasan karshe tare kuma da lashe kofin.

 

Shima babban wakilin sashen wasanni na BBC, Ian Dennis ya ce Zakarun na Italiya na da kwarin gwiwar lashe gasar, saboda yadda kungiyar ke da karfi musammna masu tsaron bayanta. Ya ce ”Sun fi kowace kungiya da ta rage a gasar karfin tsaron baya, kawo yanzu babu mai tsaron ragar da ya kai Yann Sommer, hana kwallo shiga raga a wasannin gasar ta bana’.

 

Ya kuma ce ta bangaren masu kai hari ma, kungiyar na da maciya kwallo, musamman Lautaro Martinez da a yanzu ke kan ganiyar zura kwallaye. Sannan wannan ne karo na biyu a kaka uku da kungiyar ke kai matakin wasan kusa da na karshe. Kuma kungiyar – da ke jan ragamar teburin Gasar Serie A – za ta hadu ne da Barcelona a wasan na kusa da karshe.

 

Arsenal

Kamar yadda kowa ya sani kungiyar Arsenal ce ta fitar da Real Madrid daga gasar a matakin kusa da na kusa da na karshe bayan doke ta 5-1 gida da waje. Wakilin sashen wasanni na BBC, Aled Howell na ganin kungiyar ce za ta lashe gasar. ”Duk da matsalolin da kungiyar ta fuskanta a bana, amma ta iya kai wa wannan mataki a gasar, ai kasan sun shirya wa gasar”, in ji shi.

 

”Ta fannin tsaron gida, kungiyar na da karfi sosai, haka idan ka duba ‘yan wasan gabanta hadakar Saka da Martinelli da Odegaard za su iya doke duk wata kungiya da suka ci karo da ita.

 

Kungiyar ta Mikel Arteta, wadda ke matsayi na biyu a teburin Gasar Premier ba ta taba lashe gasar ba a tarihi kuma ‘yan wasan kungiyar irinsu William Saliba da Bukayo Saka da Martin Ordegaard sun bayyana cewa suna son su rubuta sabon tarihi a kungiyar saboda haka za su yi iya yin su domin ganin cewa sun dauki gasar a karon farko a tarihin kungiyar.

 

Barcelona

Ita kungiyar kwallon kafa ta Barcelona kungiya ce wadda a yanzu babu kungiyar mai sharafinta kuma ita ce ta fitar da Borussia Dortmund daga gasar. Babban wakilin sashen wasanni na BBC, Simon Stone ya ce yana ganin kungiyar ta Sifaniya ce za ta lashe gasar, saboda yadda take kara farfadowa a baya-bayan nan. ”A yanzu kungiyar ta kara karfi musamman bayanta da tsakiya da masu kai hari”, in ji Simon Stone.

 

Kungiyar, wadda ke matsayi na daya a gasar La Liga na da zaratan matasan ‘yan wasa da ke haskakawa a fagen kwallon kafa da suka hada da Lamine Yamal da Cubersi da Balde da Fermin da Gabi da sauransu. Sanann rabon da kungiyar ta lashe gasar tun 2015 lokacin da take da zaratan ‘yanwasa irin su Lionel Messi da Luis Suares da kuma dan wasa Neymar na Brazil.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Bayan Shekaru 10 Madrid Da Barcelona Zasu Sake Yaɗuwa A Wasan Ƙarshe Na Copa Del Rey 

Next Post

Nijeriya Ta Biya Bashin Ɗaliban Da Ke Karatu A Ƙasashen Waje

Related

Kocin Super Eagle Ya Gayyaci Ahmed Musa Buga Gasar Kofin Unity A Landan
Wasanni

Kocin Super Eagle Ya Gayyaci Ahmed Musa Buga Gasar Kofin Unity A Landan

5 hours ago
Tottenham Ta Doke Manchester United A Wasan Karshe Na Europa 
Wasanni

Tottenham Ta Doke Manchester United A Wasan Karshe Na Europa 

5 hours ago
Gasar Wasanni Ta Kasa: FCT Ta Lallasa Borno Da Ci 4-1 A Wasan Farko
Wasanni

Gasar Wasanni Ta Kasa: FCT Ta Lallasa Borno Da Ci 4-1 A Wasan Farko

2 days ago
Crystal Palace Ta Lashe Kofin FA Karon Farko, Ta Doke Manchester City 1-0
Wasanni

Crystal Palace Ta Lashe Kofin FA Karon Farko, Ta Doke Manchester City 1-0

4 days ago
Me Ya Sa Manchester United Ta Fi Yin Kokari A Europa League?
Wasanni

Me Ya Sa Manchester United Ta Fi Yin Kokari A Europa League?

5 days ago
Abinda Ya Kamata Kusani Akan Wasan El Classico Na Yau
Wasanni

Abinda Ya Kamata Kusani Akan Wasan El Classico Na Yau

2 weeks ago
Next Post
Nijeriya Ta Biya Bashin Ɗaliban Da Ke Karatu A Ƙasashen Waje

Nijeriya Ta Biya Bashin Ɗaliban Da Ke Karatu A Ƙasashen Waje

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Tarwatsa Wuraren Haɗa Jabun Taki A Bauchi, An Cafke Mutum 5

‘Yansanda Sun Tarwatsa Wuraren Haɗa Jabun Taki A Bauchi, An Cafke Mutum 5

May 21, 2025
Kocin Super Eagle Ya Gayyaci Ahmed Musa Buga Gasar Kofin Unity A Landan

Kocin Super Eagle Ya Gayyaci Ahmed Musa Buga Gasar Kofin Unity A Landan

May 21, 2025
Farar Dabarar Da Tsoffin Masana’antu Ke Yi A Kasar Sin Don Tafiya Da Zamani

Farar Dabarar Da Tsoffin Masana’antu Ke Yi A Kasar Sin Don Tafiya Da Zamani

May 21, 2025
Tottenham Ta Doke Manchester United A Wasan Karshe Na Europa 

Tottenham Ta Doke Manchester United A Wasan Karshe Na Europa 

May 21, 2025
Kotu Ta Soke Umarnin Kwace Filin Asibitin Tiamin, Ta Umarci Gwamnatin Kano Ta Biya Diyyar ₦2.6bn

Kotu Ta Soke Umarnin Kwace Filin Asibitin Tiamin, Ta Umarci Gwamnatin Kano Ta Biya Diyyar ₦2.6bn

May 21, 2025
Shirye-shiryen Tinubu Suna Buɗe Hanyar Farfaɗowar Tattalin Arzikin Nijeriya – Minista

Shirye-shiryen Tinubu Suna Buɗe Hanyar Farfaɗowar Tattalin Arzikin Nijeriya – Minista

May 21, 2025
Salon “Kasa Daya Manufa Daya” Ya Dace Da “Ayyuka Goma” Na Hadin Gwiwa Da Afirka

Salon “Kasa Daya Manufa Daya” Ya Dace Da “Ayyuka Goma” Na Hadin Gwiwa Da Afirka

May 21, 2025
Sin Tana Da Karfi Wajen Tinkarar Hadari Da Kalubale A Fannoni Daban Daban

Sin Tana Da Karfi Wajen Tinkarar Hadari Da Kalubale A Fannoni Daban Daban

May 21, 2025
Sabbin Ministoci

Boko Haram: Majalisar Dattijai Ta Amince Da Kafa Sansanin Sojoji A Hong Ta Jihar Adamawa

May 21, 2025
Sin Ta Soki Yunkurin Amurka Na Hana Amfani Da Chips Kirar Kasar Sin

Sin Ta Soki Yunkurin Amurka Na Hana Amfani Da Chips Kirar Kasar Sin

May 21, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.