ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, July 17, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wace Kungiya Ce Za Ta Lashe Kofin Zakarun Turai?

by Abba Ibrahim Wada and Sulaiman
1 year ago
UEFA

Kawo yanzu dai kugiyoyin Arsenal da Inter Milan da Barcelona da kuma Paris St-Germain ne suka samu gurbi a wasan kusa da na karshe a Gasar Zakarun Turai wanda hakan ya sa yanzu tunani ya fara komawa kan kungiyar da za ta kafa tarihin lashe gasar, wadda ake sauya wa fasali kuma a ranar 24 ga watan Mayu ne za a buga wasan karshe a birnin Munich na kasar Jamus.

 

A cikin kungiyoyi hudu da suka rage a gasar a yanzu, kungiyoyin Arsenal da PSG sannan tuni masana harkokin wasanni suka fara tsokaci kan kungiyar da suke ganin za ta iya lashe gasar ta bana kasancewar a cikin kungiyoyin da suka rage a gasar Arsenal da Paris Saint German ba su taba lashe gasar ba amma kuma Inter Milan da kungiyar kwallon kafa ta Barcelona duka suna tarihin lashe gasar a baya.

ADVERTISEMENT

 

Paris St-Germain

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Bala Ya Rushe Kwamitin Gudanarwar Wikki Tourists Bayan Rashin Nasararta A Gasar NPFL

FIFA Na Nazarin Faɗaɗa Gasar Kofin Duniya Zuwa Ƙasashe 64

Kungiyar kwallon kafa ta PSG – wadda tuni ta lashe gasar League 1 ta Faransa na daya daga cikin kungiyoyin da ake ganin za su lashe gasar Zakarun Turai ta bana saboda karfin da tawagar take da shi sannan kuma kungiyar a gine take hadi da kwararren mai koyarwa, Luis Enrikue, tsohon kociyan Barcelona da Roma da tawagar kasar Spaniya, yana daya daga cikin kwararrun masu horarwa. Kungiyar za ta kara da Arsenal a wasan na kusa da karshe.

 

Wani shahararren masanin wasanni dan kasar Sifaniya, Guillem Balague na ganin PSG ce za ta lashe gasar. ”Suna da duk wani abu da ake bukata domin lashe kofin, sun iya rike kwallo, a yanzu kungiyar na da karfi, tana da masu kai hari, da na tsakiya haka ma masu tsaron baya”

 

Ya kara da cewa hanya guda da za a iya doke kungiyar ita ce idan ‘yan wasanta suka tare a baya domin tsare gida. ”In dai suka tsananta tsare gida to sai an cinye su, amma idan za su fito, to komai zai iya faruwa” a cewarsa.

 

Sai shi ma Phil McNulty, babban marubucin wasanni na BBC na ganin PSG ce za ta yi nasara a gasar. ”Suna da zaratan ‘‘yan wasa masu kai hari, misali Ousmane Dembele da Khbicha Kbaratskhelia da a yanzu ke kan ganiyarsu, ga kuma Desire Doue da Bradley Barcola wadanda matasan ‘yankwallo ne masu hazaka ”, in ji shi.

 

Inter Milan

Kungiyar kwallon kafa ta Inter Milan, kungiya ce wadda za a iya cewa babu mai kwarinta a kasar Italia domin yanayin yadda take buga wasa da yadda ba ta bari ana zura mata kwallaye a raga abu ne wanda ya kamata a kalla, sannan kuma akwai zakakuran ‘yan wasa da dama da za su taimaka wajen ganin kungiyar ta kai wasan karshe tare kuma da lashe kofin.

 

Shima babban wakilin sashen wasanni na BBC, Ian Dennis ya ce Zakarun na Italiya na da kwarin gwiwar lashe gasar, saboda yadda kungiyar ke da karfi musammna masu tsaron bayanta. Ya ce ”Sun fi kowace kungiya da ta rage a gasar karfin tsaron baya, kawo yanzu babu mai tsaron ragar da ya kai Yann Sommer, hana kwallo shiga raga a wasannin gasar ta bana’.

 

Ya kuma ce ta bangaren masu kai hari ma, kungiyar na da maciya kwallo, musamman Lautaro Martinez da a yanzu ke kan ganiyar zura kwallaye. Sannan wannan ne karo na biyu a kaka uku da kungiyar ke kai matakin wasan kusa da na karshe. Kuma kungiyar – da ke jan ragamar teburin Gasar Serie A – za ta hadu ne da Barcelona a wasan na kusa da karshe.

 

Arsenal

Kamar yadda kowa ya sani kungiyar Arsenal ce ta fitar da Real Madrid daga gasar a matakin kusa da na kusa da na karshe bayan doke ta 5-1 gida da waje. Wakilin sashen wasanni na BBC, Aled Howell na ganin kungiyar ce za ta lashe gasar. ”Duk da matsalolin da kungiyar ta fuskanta a bana, amma ta iya kai wa wannan mataki a gasar, ai kasan sun shirya wa gasar”, in ji shi.

 

”Ta fannin tsaron gida, kungiyar na da karfi sosai, haka idan ka duba ‘yan wasan gabanta hadakar Saka da Martinelli da Odegaard za su iya doke duk wata kungiya da suka ci karo da ita.

 

Kungiyar ta Mikel Arteta, wadda ke matsayi na biyu a teburin Gasar Premier ba ta taba lashe gasar ba a tarihi kuma ‘yan wasan kungiyar irinsu William Saliba da Bukayo Saka da Martin Ordegaard sun bayyana cewa suna son su rubuta sabon tarihi a kungiyar saboda haka za su yi iya yin su domin ganin cewa sun dauki gasar a karon farko a tarihin kungiyar.

 

Barcelona

Ita kungiyar kwallon kafa ta Barcelona kungiya ce wadda a yanzu babu kungiyar mai sharafinta kuma ita ce ta fitar da Borussia Dortmund daga gasar. Babban wakilin sashen wasanni na BBC, Simon Stone ya ce yana ganin kungiyar ta Sifaniya ce za ta lashe gasar, saboda yadda take kara farfadowa a baya-bayan nan. ”A yanzu kungiyar ta kara karfi musamman bayanta da tsakiya da masu kai hari”, in ji Simon Stone.

 

Kungiyar, wadda ke matsayi na daya a gasar La Liga na da zaratan matasan ‘yan wasa da ke haskakawa a fagen kwallon kafa da suka hada da Lamine Yamal da Cubersi da Balde da Fermin da Gabi da sauransu. Sanann rabon da kungiyar ta lashe gasar tun 2015 lokacin da take da zaratan ‘yanwasa irin su Lionel Messi da Luis Suares da kuma dan wasa Neymar na Brazil.

Zakarun Turai
Abba Ibrahim Wada
Website |  + posts Bio
  • Abba Ibrahim Wada
    Ronaldo Da Ƴanwasan Da Suka Buga Kofin Duniya Na Ƙarshe A Rayuwarsu
  • Abba Ibrahim Wada
    Ko Ka San Dalilin Da Ya Sa Chana Da Indiya Ba Sa Buga Kofin Duniya?
  • Abba Ibrahim Wada
    Gwamnatin Kaduna Ta Yaba Wa NSA Kan Shirin Samar Da Dakarun Tsaron Daji
  • Abba Ibrahim Wada
    Lampard Zai Ci Gaba Da Zama A Coventry City
Zakarun Turai
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Pew: Sin Ta fi Amurka Samun Amincewar Al’ummun Duniya
  • Sulaiman
    Sin Ta Fitar Da Tsarin Sanya Ido Don Inganta Muhalli Da Muhallin Halittu Na Shekarar 2026 Zuwa 2030
  • Sulaiman
    Nazari Game Da Damammakin Da Sin Ta Samar Cikin Rahoton Ci Gaban Tattalin Arzikinta Na Rabin Farkon Shekara
  • Sulaiman
    Gwamna Bala Ya Rushe Kwamitin Gudanarwar Wikki Tourists Bayan Rashin Nasararta A Gasar NPFL

MASU ALAKA

Gwamna Bala Ya Rushe Kwamitin Gudanarwar Wikki Tourists Bayan Rashin Nasararta A Gasar NPFL
Wasanni

Gwamna Bala Ya Rushe Kwamitin Gudanarwar Wikki Tourists Bayan Rashin Nasararta A Gasar NPFL

July 16, 2026
FIFA Na Nazarin Faɗaɗa Gasar Kofin Duniya Zuwa Ƙasashe 64
Wasanni

FIFA Na Nazarin Faɗaɗa Gasar Kofin Duniya Zuwa Ƙasashe 64

July 12, 2026
Harry Kane: Lashe Kofin Duniya Ya Fi Mini Muhimmanci Fiye da Takalmin Zinare
Wasanni

Harry Kane: Lashe Kofin Duniya Ya Fi Mini Muhimmanci Fiye da Takalmin Zinare

July 11, 2026
Next Post
Nijeriya Ta Biya Bashin Ɗaliban Da Ke Karatu A Ƙasashen Waje

Nijeriya Ta Biya Bashin Ɗaliban Da Ke Karatu A Ƙasashen Waje

LABARAI MASU NASABA

Falalar Salatut Tasbihi

Falalar Salatut Tasbihi

July 17, 2026
A Baya Ba A San Jihar Kano Da Harkar Daba Ba – Tsohon Shugaban NAHCON

A Baya Ba A San Jihar Kano Da Harkar Daba Ba – Tsohon Shugaban NAHCON

July 17, 2026
Direba Ya Hallaka Ɗalibar Jami’ar Kiwon Lafiya Ta Azare, Ya Gudu

Direba Ya Hallaka Ɗalibar Jami’ar Kiwon Lafiya Ta Azare, Ya Gudu

July 17, 2026
Wasu Sassan Birnin Abuja Na Fuskantar Barazanar Rusau

Wasu Sassan Birnin Abuja Na Fuskantar Barazanar Rusau

July 17, 2026
Mata Manoma Sun Gina Gada, Rijiyar Burtsatse A Danbare, Kano

Mata Manoma Sun Gina Gada, Rijiyar Burtsatse A Danbare, Kano

July 17, 2026
Yadda NDLEA Ke Fatattakar Dillalan Miyagun Kwayoyi Na Kudancin Amurka

Yadda NDLEA Ke Fatattakar Dillalan Miyagun Kwayoyi Na Kudancin Amurka

July 17, 2026
Gwamnan Da Bai Taba Samun Mulkin Jihar Kano Ba

Gwamnan Da Bai Taba Samun Mulkin Jihar Kano Ba

July 17, 2026
An Ceto Wasu Mutane Huɗu Da Aka Sace A Kogi

An Ceto Wasu Mutane Huɗu Da Aka Sace A Kogi

July 17, 2026
NPA Ta Tara Kudin Shiga Naira Biliyan 758.2 A 2024

Dalilin Da Ya Sa Kungiyar NCTR Ta Jinjina Wa Shugaban NPA

July 17, 2026
Yunkurin Dauda Lawal Na Bunkasa Bangaren Ma’adanan Jihar Zamfara

Yunkurin Dauda Lawal Na Bunkasa Bangaren Ma’adanan Jihar Zamfara

July 17, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.