ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bayan Jinkiri Da Dimbin Hasashe Abba Kabir Yusuf Ya Rungumi Tafiyar Tinubu

by Azu Ishiekwene and Rabi'u Ali Indabawa
7 months ago
Abba

Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, a karshe ya yanke alaka da Rabiu Musa Kwankwaso, surukinsa, jagoransa kuma uban gidansa a siyasa.

Yusuf ya kasance a karkashin inuwar Kwankwaso tsawon kusan shekaru 25, inda ya rike mukamai daban-daban, ciki har da mukamin kwamishina a Jihar Kano, har zuwa shekarar 2023, lokacin da Kwankwaso ya tsayar da shi takarar gwamna, duk da kasancewar akwai wasu ‘yan takara mafi shahara.

  • Rikicin Iran Da Amurka: Gabas Ta Tsakiya Ta Ɗauki Zafi
  • Kasuwar Musayar ‘Yan Kwallo: Kante Ya Kammala Komawa Fenerbahce

Yusuf ya bi ubangidansa Kwankwaso daga PDP zuwa APC, daga nan ya koma PDP, sannan zuwa NNPP. Wannan hadin gwiwa ta kasance wadda aka jarraba kuma ta tabbatar da kanta tsawon lokaci.

ADVERTISEMENT

Irin abin da ‘yan siyasa kadai ke iya watsarwa sannan su murmure daga girgizar da ya haifar cikin kankanin lokaci ko ma ba tare da bata lokaci ba.

Hanyar Zama Namiji Mai (’yancin kai)

LABARAI MASU NASABA

Buni Ya Nuna Kwarewarsa Ta Diflomasiyya

Shin Tinubu Ya Tabbatar Da Sauke Ribadu Daga Mukaminsa?

A ranar Litinin, 26 ga Janairu, Yusuf ya koma kan abin da shi da uban gidansa a siyasa suka taba kin kusanta, wato abin da tsohon Gwamna Abdullahi Ganduje wani tsohon abokin tafiyar Kwankwaso na dogon lokaci wanda daga baya ya kauce masa ya kuma jefar da hula ya aikata.

Tun bayan da ya samu nasarar zabe mai cike da cece-kuce ta hukuncin Kotun Koli a watan Janairun 2024 hukuncin da ya soke na Kotun Zabe da kuma Kotun Daukaka Kara magoya baya, masoya da masu karfafa gwiwa suka fara rada wa gwamnan kunne da ya ajiye kwalbar shayarwa, ya tsaya da kafafunsa da kansa.

Idan aka waiwayi al’amura, wannan dole ne ya kasance hukunci ne na ko a ci ko a mutu ga Yusuf, wanda aka fi sani da “Abba Gida-Gida.” Wani mawuyacin hali ne

Amma daga karshe, ya tsallaka kogin Rubicon, ya kubuta daga abin da mutane da dama ke kallon a matsayin wa’adin mulki na uku na surukinsa a Fadar Gwamnatin Kano.

Amon Martani Daga Roma

A cikin abin da ya yi kama da amo daga tsohuwar Roma, Kwankwaso ya ayyana ranar 23 ga Janairu ranar da Yusuf ya sauya sheka a matsayin Ranar Cin Amana ta Duniya. Idan Kano ta zama Roma, shin Yusuf zai zama sabon Julius Caesar, Kwankwaso kuma Pompey? Kamar yadda Caesar ya yi a zamanin Roma, gwamnan ya bijire wa gargadin kada ya tsallaka kogin Rubicon abin da a wancan lokaci ya kasance babban matakin shelanta yaki.

Amma ganin cewa iska ta iko na tura jirgin Yusuf gaba, yayin da Kwankwaso ke cikin hunturun Pompey, gwamnan ya zabi lokaci mafi rauni don kai hari.

Natsuwar Da Ke Cike Da Fargaba

Abin mamaki, Kano na cikin kawaici a halin yanzu. Motsi na Kwankwasiyya mai cike da tsananin biyayya, rundunar masu sanya jar hula da ke daukar Kwankwaso a matsayin gwarzo, jar hular kuma alamar aminci kamar sun karbi abin da suka kira cin amanar Yusuf kamar dai yadda suka yi a lokacin Ganduje a baya: suna jira ne kawai, cikin natsuwa mai cike da fargaba.

A cikin duniyar siyasa mai cike da kifayen Shark, kare kai shi ne doka ta farko. Me nake samu a ciki? Shin akwai hanyar da zan bi in samu wa’adi na biyu, musamman ganin jita-jitar cewa Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Barau Jibrin, na da burin tsayawa takara? Ko kuwa an tanadar min mafita lafiya idan na bar mulki? Manyan masu ruwa da tsaki su kan fara da tabbatar da tasu maslahar, daga bisani ne ake tattauna muradun mabiyansu.

Mataki Na Gaba Ga Al’ummar Kano?

Me ke gaba? Kano sau da yawa na karya ka’idojin siyasa. Siyasar jihar tana da zurfi, tana da halin bijirewa al’ada cikin hadari, amma kuma tana da tasiri mai nauyi. Wannan ne ya sa jam’iyyar NEPU ta Aminu Kano ta doke jam’iyyar NPC mai goyon bayan masu mulki, kuma ya sa PRP ke doke NPN a kai a kai.

A shekarar 2003, jam’iyyar ANPP ta Ibrahim Shekarau ta doke jam’iyyar PDP mai karfi a fadin kasa karkashin Kwankwaso, kafin Kano ta haifi motsin jar hula mai tsananin biyayya ko da ba tare da wani takamaiman dalili ba bayan shekaru takwas.

Yanzu haka, da yiwuwar sake jeri na siyasa inda Yusuf, Ganduje da Shekarau za su kasance a bangare guda, yayin da Kwankwaso ke a daya gefen, an riga an jefa kuri’ar kaddara.

“Shirme!” in ji wani aminin Kwankwaso. “Idan Kano ta yi yunkurin taka rawa a zaben gwamna na 2027, to sauyin shekar Yusuf na iya zama abin da zai rufe masa makomar siyasa gaba daya. Tunanin cewa kasancewa a jam’iyyar da ke kan mulki tabbacin nasara ce, tana iya zama kuskure mai hallakarwa ba gare shi kadai ba, har da sauran gwamnonin da suka sauya sheka.

Jar Hulata

Kusan nan take bayan sauyin shekarsa, an fara bayyana cewa Yusuf yana da tabbacin samun tikitin takarar gwamna na APC a zaben shekara mai zuwa. Tun kafin ya bar NNPP, yana da hakkin fifiko (right of first refusal) kan tikitin jam’iyyar. Kuma har yanzu yana sanye da jar hularsa.

Tuni ma an fara ganin hadakar jan hular da alamar Tinubu. Shin Yusuf zai tafi APC tare da Kwankwaso? Kada wani ya yi mamaki idan hakan ta faru, duk da hayaniyar zargin cin amana. ‘Yan siyasa ba lallai su kasance masu nufin abin da suke fada ba.

Abin da ke gaba na yi wa kowa alkawarin zama abin sha’awa da kuma daukar hankali matuka.

Ishiekwene shi ne Babban Edita (Editor-In-Chief) na jaridar LEADERSHIP, kuma marubucin littafin ‘Writing for Media and Monetising It.

Abba
Azu Ishiekwene
+ posts Bio
  • Azu Ishiekwene
    https://hausa.leadership.ng/author/azu-ishiekwene/
    Muhammadu Sa’ad Abubakar III: Sarkin Da Ya Dace Da Kowane Zamani
  • Azu Ishiekwene
    https://hausa.leadership.ng/author/azu-ishiekwene/
    Su Wa Ke Fatattakar Obi Da Kwankwaso?
  • Azu Ishiekwene
    https://hausa.leadership.ng/author/azu-ishiekwene/
    Wayoyin Wutar Lantarkin Adelabu Sun Zama Tamkar Igiyoyin Shanya
  • Azu Ishiekwene
    https://hausa.leadership.ng/author/azu-ishiekwene/
    Wayoyin Wutar Lantarkin Adelabu Sun Zama Tamkar Igiyoyin Shanya
Abba
Rabi'u Ali Indabawa
+ posts Bio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƙungiya Ta Gudanar Da Zaɓen Sabbin Shugabanninta A Abuja
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Jihar Katsina Da UNICEF Sun Ceto Rayuwar Yara Ta Hanyar Samar Da Abinci Mai Gina Jiki
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Yadda Tinubu Ya Kashe Naira Biliyan 37.64 A Tafiye-tafiye
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ta’addaci: Mutum 14,500 Sun Bace A Arewa Maso Gabas

MASU ALAKA

Zanga-Zanga: Gwamnatin Yobe Ta Bayar Da Umarnin Rufe Makarantun Jihar
Bakon Marubuci

Buni Ya Nuna Kwarewarsa Ta Diflomasiyya

August 28, 2026
An Kusa Ceto Ɗaliban Neja Da Aka Sace – Ribadu
Bakon Marubuci

Shin Tinubu Ya Tabbatar Da Sauke Ribadu Daga Mukaminsa?

August 28, 2026
Kwairanga Ya Kafa Tarihi A Shugabancin Hukumar Kula Da Kasuwar Hannun Jari Ta Nijeriya
Bakon Marubuci

Kwairanga Ya Kafa Tarihi A Shugabancin Hukumar Kula Da Kasuwar Hannun Jari Ta Nijeriya

July 24, 2026
Next Post
Arewa Maso Gabashin Jigawa: Abokan Babandede Sun Dauki Harama

Arewa Maso Gabashin Jigawa: Abokan Babandede Sun Dauki Harama

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.